Shugaban Lebanon, Joseph Aoun, ya nemi da kasar ta gudanar da shawarwari kai tsaye da daddiyar abokiyar gabarta Isra’ila, tun bayan da yaki ya barke wata guda da ya shige, a cikin wata dayan ne Isra’ila ta tilastawa ‘yan kasar lebanon fiye da milyan daya barin muhallansu, ta rusa wani sashe na Beiruit, wanda ya sabunta rikici na banbanci tsakanin yan kasar.
Yanzu, daga karshe da Prime Minustan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya amince da a gudanar da shawarwarin sulhu, masana da masu sharhi sunce Lebanon tana cikin yanayi na rashin karfin daukar wani mataki da zai yi tasiri.
Kungiyar Hezbollah, wacce take artabu da Isra’ila a kudancin kasar, bata goyon bayan a gudanar da shawarwarin ido da ido da Isra’ila, wanda ya jefa shakku kan ko zata amince da duk wata yarjejeniyar tsagaita wuta da Lebanon ta kulla.
“Shawarwari da za’a yi tsakanin Lebanon da Isra’ila a gaskiya bashi da ma’ana, domin wadanda za su gudanar da shawarwarin a madadin Lebanon, basu da wani iko ko tasiri na gudanar da shawarwarin,” kamar yadda wani jami’in kasar wanda yake da kusanci da kungiyar Hezbollah ya gayawa Manema labarai.


