Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu
Published: December 10, 2025 at 4:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Farfesa Wole Soyinka ya yi gargaɗi ga Shugaba Bola Tinubu kan yadda ake gudanar da tsaro da kuma amfani da jami’an gwamnati wajen kare wasu ‘yan tsiraru masu kusanci da fada.

Yayin bikin bayar da kyaututtuka na Wole Soyinka Centre for Investigative Journalism a Legas, a wani bidiyo da ya yadu, Soyinka ya ce ya yi mamakin ganin “babbar rundunar tsaro” da aka bai wa Seyi Tinubu, ɗan shugaban ƙasa, a Ikoyi.

Ya bayyana cewa yawan jami’an tsaron da ya gani “ya isa ya mamaye ƙaramar ƙasa,” lamarin da ya sa ya tuntubi mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin neman bayani.

Soyinka ya ce bai dace ‘ya’yan shugabanni su gaji karfin gwamnati ko su yi yawo da tsaro fiye da kima ba, yayin da ƙasar ke fama da hare-hare, garkuwa da mutane da rashin tsaro a sassa da dama.

Ya ƙara da cewa irin wadannan albarkatun tsaro ya fi dacewa a tura su wuraren da ake bukata, ba wajen kare masu gata ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci

Karin Labarai Masu Alaka

Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon Wasanni
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.