Tawagar Asusun Ba da Lamuni ta Duniya ta IMF isa kasar Kenya don tattaunawa kan sabon shirin lamuni, a cewar gwamnati da hukumomin IMF.
Hukumomin kasar suna kokarin tsara wani sabon shirin ba da lamuni bayan karewar yarjejeniyar da aka cimma a baya na dalar Amurka biliyan 3.6 a watan Afrilu kuma bangarorin biyu sun yi wata tattaunawa a Nairobi da Washington.
“An tsara tawagar IMF za ta ziyarci Kenya daga ranar 24 ga Fabrairu zuwa 4 ga Maris 2026 don ci gaba da tattaunawa kan tsarin da zai maye gurbin wanda zai kare da nufin tallafawa manyan tsare-tsare da kuma Yiwuwar bayar da taimakon kudi,” in ji gwamnatin a cikin wani rahoto na Eurobond da aka fitar a bainar jama’a da yammacin ranar Talata.
Tattaunawar dai na da nufin tabbatar da cewa duk wani sabon shirin ya dace da “kudurin kasafin kudi da na tattalin arziki” na kasar Kenya, tare da tallafa wa tattalin arzikin kasa da kasa, in ji gwamnatin a cikin hasashen, wani bangare na bayar da dala biliyan 2.25 a makon da ya gabata.


