Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin
Published: December 7, 2025 at 10:13 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 8, 2025

Shugaba Tinubu ya yaba wa sojojin Najeriya kan kare demokuraɗiyya a Jamhuriyar Binin.

Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya jinjinawa rundunar sojin ƙasar bisa gaggawar da ta yi wajen amsa kiran gwamnatin Jamhuriyar Binin domin taimakawa wajen kare tsarin mulkinsu na dimokuraɗiyya, bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi a ƙasar da safiyar Lahadi.

A cewar fadar shugaban ƙasa, gwamnatin Binin ta aikawa Najeriya da buƙatu biyu na gaggawa, ta hanyar Ma’aikatar Harkokin Wajen ƙasar, tana neman a turo da jiragen yaƙin saman Najeriya domin kwace tasoshin da sojojin da suka yi juyin mulkin suka mamaye, ciki har da Talabijin na ƙasa da kuma wani sansanin soja.

Najeriya ta amsa wannan kira nan take, inda Shugaba Tinubu ya umarci rundunar sojin sama ta NAF ta shiga sararin samaniyar Binin domin kawar da barazanar.

Haka kuma gwamnatin Binin ta roƙi a tura ƙarin jiragen leƙen asiri da kuma sojojin ƙasa na Najeriya, domin taimaka musu a ayyukan tsaro da kariyar manyan cibiyoyin gwamnati a ƙarƙashin jagorancin hukumomin tsaron Binin.

Babban Hafsan Sojin Najeriya, Janar Olufemi Oluyede, ya tabbatar da cewa an kammala dukkan bukatun da ƙasar Binin ta nema, ciki har da zuwan sojojin Najeriya cikin ƙasar.

Yunƙurin juyin mulkin dai ya faru ne bayan wasu sojoji ƙarƙashin jagorancin Kanar Pascal Tigri sun mamaye gidan talabijin na ƙasar, inda suka bayyana cewa sun hambarar da gwamnatin Shugaba Patrice Talon tare da dakatar da muhimman hukumomin dimokuraɗiyya.

Sai dai da taimakon dakarun Najeriya, jami’an gwamnati masu biyayya ga Shugaba Talon sun kwace tashar Talabijin ɗin da sauran wuraren da aka mamaye, lamarin da ya kawo ƙarshen yunkurin juyin mulkin.

Da yake martani bayan tabbatar da dawowar tsarin dimokuraɗiyya, Shugaba Tinubu ya yaba wa sojojin Najeriya bisa rawar da suka taka.

“A yau, rundunar sojin Najeriya ta tsaya kai da fata wajen kare tsarin mulki a Jamhuriyar Binin bisa gayyatar gwamnatin ƙasar. Sun yi aiki bisa ka’idojin yarjejeniyar ECOWAS kan dimokuraɗiyya da kyakkyawan mulki,” in ji Shugaba Tinubu.

Ya ƙara da cewa Najeriya za ta ci gaba da goyon bayan gwamnati da al’ummar Binin wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciya hankali a yankin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba”
Next Post: Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s

Karin Labarai Masu Alaka

Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.