Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Published: December 13, 2025 at 10:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gidauniyar Alhaji Dahiru Barau Mangal, wato Mangal Foundation, ta fara gudanar da tiyatar cutar Hernia da Hydrocele kyauta ga mutane sama da 800 a jihar Katsina.

An fara aikin ne a Babban Asibitin Katsina ranar Juma’a 12 ga Disamba, 2025, bayan kammala tantance mutanen da ke fama da cututtukan a kwanakin baya.

A yayin tantancewar, an gano mutane da dama da ke bukatar tiyata, inda gidauniyar ta dauki nauyin aikin kyauta, ba tare da wadanda suka amfana sun biya ko sisi ba.

Da yake jawabi yayin fara aikin, ɗaya daga cikin ‘yan kwamitin amintattu na gidauniyar, Alhaji Hussaini Kabir, ya bayyana cewa za a ci gaba da gudanar da tiyatar har zuwa ranar Lahadi.

Alhaji Hussaini Kabir ya kara da cewa, bayan an yi wa marasa lafiya aikin, gidauniyar za ta ci gaba da daukar nauyin kulawa da su da magunguna har zuwa lokacin da za a sallame su daga asibiti.

Ya bayyana cewa, a lokacin tantancewar, an duba daruruwan mutane masu fama da matsalolin lafiya daban-daban, inda da yawa daga cikinsu aka ba su magunguna kyauta aka kuma sallame su.

Alhaji Kabir ya jaddada cewa wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke gudanar da irin wannan aiki ba, yana mai cewa a duk shekara ana shirya irin wannan aiki domin tallafawa al’umma.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin sun bayyana godiya da addu’o’i ga shugaban gidauniyar, bisa wannan tallafi.

Sun kuma yi kira ga gwamnatoci, kamfanoni da masu hannu da shuni da su yi koyi da gidauniyar wajen tallafa wa marasa galihu a fadin kasar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri
Next Post: Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.