Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Published: December 13, 2025 at 10:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gidauniyar Alhaji Dahiru Barau Mangal, wato Mangal Foundation, ta fara gudanar da tiyatar cutar Hernia da Hydrocele kyauta ga mutane sama da 800 a jihar Katsina.

An fara aikin ne a Babban Asibitin Katsina ranar Juma’a 12 ga Disamba, 2025, bayan kammala tantance mutanen da ke fama da cututtukan a kwanakin baya.

A yayin tantancewar, an gano mutane da dama da ke bukatar tiyata, inda gidauniyar ta dauki nauyin aikin kyauta, ba tare da wadanda suka amfana sun biya ko sisi ba.

Da yake jawabi yayin fara aikin, ɗaya daga cikin ‘yan kwamitin amintattu na gidauniyar, Alhaji Hussaini Kabir, ya bayyana cewa za a ci gaba da gudanar da tiyatar har zuwa ranar Lahadi.

Alhaji Hussaini Kabir ya kara da cewa, bayan an yi wa marasa lafiya aikin, gidauniyar za ta ci gaba da daukar nauyin kulawa da su da magunguna har zuwa lokacin da za a sallame su daga asibiti.

Ya bayyana cewa, a lokacin tantancewar, an duba daruruwan mutane masu fama da matsalolin lafiya daban-daban, inda da yawa daga cikinsu aka ba su magunguna kyauta aka kuma sallame su.

Alhaji Kabir ya jaddada cewa wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke gudanar da irin wannan aiki ba, yana mai cewa a duk shekara ana shirya irin wannan aiki domin tallafawa al’umma.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin sun bayyana godiya da addu’o’i ga shugaban gidauniyar, bisa wannan tallafi.

Sun kuma yi kira ga gwamnatoci, kamfanoni da masu hannu da shuni da su yi koyi da gidauniyar wajen tallafa wa marasa galihu a fadin kasar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri
Next Post: Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.