Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu
Published: January 9, 2026 at 7:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sanar da kama mutane hudu tare da kwato dabbobi masu yawa da ake zargin an sace su, a wani yunkuri na dakile satar dabbobi da fashin shanu a fadin jihar.

A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, samamen ya gudana ne da hadin gwiwar ’yan sa-kai da mafarauta.

A yayin ayyukan, an kama wasu matasa a yankunan Yamaltu-Deba, Kaltungo da Balanga, tare da kwato shanu biyu, tumaki 274, awaki 54 da jaki guda.

Rundunar ta ce an gano wasu daga cikin dabbobin nan take daga hannun masu su, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano sauran masu dabbobin da kuma cafke wadanda ke tsere.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya yaba da hadin gwiwar al’umma, tare da jaddada kudirin rundunar na yakar satar dabbobi da sauran laifuka. Ya kuma bukaci jama’a da su rika bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

’Yan sanda sun tabbatar da cewa za a gurfanar da dukkan wadanda aka kama gaban kotu bayan kammala bincike.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari
Next Post: Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta Tsaro
EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.