Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta sanar da kama mutane hudu tare da kwato dabbobi masu yawa da ake zargin an sace su, a wani yunkuri na dakile satar dabbobi da fashin shanu a fadin jihar.
A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, samamen ya gudana ne da hadin gwiwar ’yan sa-kai da mafarauta.
A yayin ayyukan, an kama wasu matasa a yankunan Yamaltu-Deba, Kaltungo da Balanga, tare da kwato shanu biyu, tumaki 274, awaki 54 da jaki guda.

Rundunar ta ce an gano wasu daga cikin dabbobin nan take daga hannun masu su, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano sauran masu dabbobin da kuma cafke wadanda ke tsere.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya yaba da hadin gwiwar al’umma, tare da jaddada kudirin rundunar na yakar satar dabbobi da sauran laifuka. Ya kuma bukaci jama’a da su rika bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

’Yan sanda sun tabbatar da cewa za a gurfanar da dukkan wadanda aka kama gaban kotu bayan kammala bincike.


