‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba
A wata rahoto daga kafafen yada labarai na MoroccoWorldNews ta wallafa ta cewa lamarin gasar cin kofin duniya ta Qatar ta 2022 ya sake maimaita kansa a lokacin gasar cin kofin kasashen Afirka ta 2025 (AFCON) da ake gudanarwa a Morocco, yayin da magoya baya ke fafutukar samun tikitin wasa saboda hanyoyin sadarwa da ke sayar da su ba bisa ka’ida ba.
‘Yan sandan Morocco sun bude wani bincike na shari’a kan siyar da tikitin AFCON ba bisa ka’ida ba a karkashin kulawar ofisoshin masu gabatar da kara na gwamnati.
Hukumomi sun ce ana zargin mutane takwas da hannu a cinikin tikitin wasa ba bisa ka’ida ba.
An bayyana lamarin bayan da sassan sa ido kan bayanai na ‘yan sandan kasa suka gano rubuce-rubuce a shafukan sada zumunta da ke bayar da tikitin sayarwa ta hanyoyin da ba a ba da izini ba.
Bayan binciken fasaha da aikin filin wasa, ‘yan sanda sun sami damar gano wadanda ake zargin.
Sannan suka gudanar da ayyukan tsaro a birane da dama, ciki har da Rabat, Temara, Agadir, Salé, Marrakech, da Mohammedia, wanda ya kai ga kama wadanda ake zargin.
Yanzu haka ana binciken mutanen da aka kama domin tantance dukkan yanayi da kuma asalin lamarin.
Hukumomin sun kuma tabbatar da cewa ana ci gaba da bincike don gano da kuma kama wasu mutanen da ke da hannu a lamarin.
Masoya da dama sun yi ta kai-kawo a shafukan sada zumunta kwanan nan suna korafin rashin samun tikitin wasa, inda mutanen da suka sayi tikitin da yawa daga yanar gizon hukuma suka sake sayar da su kan farashi mai tsada a kasuwar bayan fage.
Wasu suna sayar da tikitin da aka masa farashi a MAD 150 ($15) kan MAD 1,500 ($150), yayin da tikitin da Mai farashin MAD 500 ake sayar da shi a kasuwar bayan fage kan MAD 3,500 zuwa MAD 4,500.
Farashin da aka yi ya wuce gona da iri ya hana magoya baya da dama halartar bikin bude gasar da kuma wasan farko na Morocco da Comoros. Sakamakon haka, dubban kujeru a filin wasa na Moulay Abdellah da aka gyara a Rabat sun kasance babu kowa.
Masu amfani da shafukan sada zumunta da dama sun nuna kujeru kusan 10,000 ba kowa a filin wasa mai kujeru 70,000. Masoya suna fatan hukumomi za su gano mafita da za ta ba su damar halartar wasannin Atlas Lions da kuma yi musu maraba.


