Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya
Published: March 9, 2026 at 6:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan ta’adda sun hallaka a kalla sojoji 12 da farar hula uku a wani hari da suka kai cikin dare a arewa maso gabashin Nigeria, a cewar majiyoyi daga sojoji da kuma mazauna wurin ranar Litinin.

Harin ya auku a garuruwan Kukawa da Dalwa a jihar Borno, da kuma Goniri a jihar Yobe kuma ya biyo bayan wani harin da aka kai kwanaki garin Ngoshe.

Kungiyar Boko Haram sun farwa Kukawa kafin wayewar garin ranar Litinin, suka durfafi sansanin soji dake wajen, inda aka shafe sa’o’i uku ana musayar wuta. Daga bya sojoji sun yi nasara, amma kwamandan rundunar da wasu sojoji biyar sun rasa rayukan su. Dan majalisa mai wakiltar Kukawa, Karta Ma’aji, ya tabbatar da aukuwar harin.

A Dalwa kuma ‘yan ta’addan sun kashe sojoji biyu da farar hula uku, sannan suka kona gidaje 250. A Goniri kuma da ke jihar Yobe, nan ma sun kai hari sansanin soji, inda suka hallaka sojoji hudu, suka kuma kone motocin wurin.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100
Next Post: Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa

Karin Labarai Masu Alaka

Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
  • An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.