Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya”
Published: December 5, 2025 at 5:18 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Jajircewa da muka nuna a baya ita ta sa Shugaba Bola Ahmad Tinubu, ya sake dauko ni don na ja ragamar ma’aikatar tsaro ta kasa. Tsarin aikin mu shine, ba nuna banbanci na addini ko kabilanci, haka kuma ba sani ba sabo wajen gabatar da aiki.

Mu duka ‘yan Najeriya ne sai mun hada hannu da tunanin mu waje daya sannan zamu iya samun zaman lafiya. Babban abun da yasa muke yin nasara shi ne son kasa da kishin ci gabanta.

Zamu hada kan dukannin jami’an tsaro waje daya, don ganin an yi aiki tare da samar da mafita ga kasa. A can baya mun fuskanci kalubale na rashin hadin kai, amma yanzu burin mu shine mu taho da kowa a cikin sabuwar tafiya.

Shugaban kasa ya dau alwashin bamu damar yin aiki ba tare da wata damuwa ba, ya kuma ce zai bamu dukkan wata gudunmawa da muke nema wajen kawo karshen ta’addanci a kasar. Na tabbatar ma sojoji wannan kudurin na aiki tukuru don kawo karshen matsalolin rashin tsaro a kasar.

Babban abun da muke nema shi ne gudunmawar Allah da ta jama’a wajen taya mu da addu’a da bada bayanan siri a duk lokacin da aka ga wani abu da bai yi tsari da zaman takewar al’ummah ba.

Duk wanda yake tare da Allah to zai ga nasara a cikin al’amuransa, don haka zamu yi aiki da kowa a wannan sabon matsayi.

Bamu da wani shiri na yin sulhu da ‘yan ta’adda, don kuwa basu da hujja ta kama talakawa da basu ji basu gani ba, mun dau damarar yakar su haikan, daga nan har illa-masha Allah.

Gwamnatin mu a shirye take taga mun kawo karshen ‘yan ta’adda a kowane hali, don haka muna neman addu’o’in ‘yan Najeriya a kowane hali da neman nasara akan duk bata gari.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/1st-Report-Defence-Minister-Christopher-Musa-.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto
Next Post: CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.