Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa
Published: December 9, 2025 at 7:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Gwamnonin jihohin arewa ta Naɗa Ezekiel Gomos a matsayin babban darakta don karfafa haɗin kan yankin

Kungiyar gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) ƙarƙashin jagorancin Shugabanta kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ta amince da naɗin Mista Ezekiel Gomos, OFR, a matsayin Babban daraktan sakatariyar ƙungiyar.

Naɗin dai ya yi daidai da sabbin alƙawuran da ƙungiyar ta ɗauka na ƙarfafa ayyukan hukumominta da inganta haɗin kai a tsakanin jihohin Arewa 19 wajen tinkarar ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

A cewar ƙungiyar, samar da ofishin Babban Daraktan wani kyakkyawan mataki ne na mayar da Sakatariyar ya zuwa cibiya mai inganci wajen haɗa kai da inganta manufofi, da aiki tare da kuma samar da tsare-tsaren ci gaba na dogon zango.

Mista Gomos, wadda tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Filato ne, ƙwararre ne a fannin tattalin arziƙi, siyasa da aikin gwamnati, da kuma inganta harkokin mulki, da bunƙasa kamfanoni masu zaman kansu da kuma ciyar da jama’a gaba.

Ƙwarewarsa ta haɗa da manyan ayyuka a manyan cibiyoyi masu tasiri irin su New Nigeria Development Company (NNDC) da kuma Hukumar Shirya Jarrabawa ta Yammacin Afirka (WAEC).

Bugu da ƙari, ya kasance ƙwararren mai bada shawara kuma shugaban tsangaya a Makarantar Kasuwanci ta Jos (JBS), makarantar data mayar da hankali wajen bunƙasa harkokin kasuwanci, horas da shugabanni da tsare-tsaren manufofi.

Mista Gomos ya shafe kusan shekaru ashirin yana aiki a Cibiyar Nazarin Siyasa da Dabaru ta Kasa (NIPSS) dake Kuru, inda ya bada gudummawa wajen horar da manyan shugabanni a faɗin Najeriya ta fuskar manufofi, dabaru da ci gaban ƙasa.

Sauran harkokin karatu na sabon Babban Daraktan sun haɗa da digiri na ɗaya dana biyu da ya yi a jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya da kuma Jami’ar East Anglia ta kasar Birtaniya.

Har ila yau mamba ne a wasu manyan cibiyoyi na duniya, ciki har da Hubert Humphrey Fellowship (na Jami’ar Minnesota) da Chevening Scholarship na Birtaniya da kuma kasancewarsa mamba a hukumar ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya (UNDP Fellowship) a Cibiyar Horaswa ta Ƙungiyar Ƙwadago ta Duniya (ILO) a Turin.

Gomos ya halarci manyan horaswar shugabanci a Makarantun Harvard Kennedy, da Jami’ar Chicago Booth School of Business, da Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Durham.

Da yake gabatar da takardar naɗin, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Mista Gomos ya yi amfani da ƙwarewarsa ta fannin jagoranci dabaru, ci gaban cibiyoyi da tsare-tsare don ƙarfafa sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin ta Arewa zuwa wata katafariyar dandalin haɗin gwiwar tsaro da tattalin arziƙin yankin da kuma ci gaba mai ɗorewa a faɗin Arewa.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewan ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa naɗin zai haifar da wani sabon yanayi na zurfafa haɗin gwiwa, da ingantaccen haɗin kai da kuma samar da matakan da suka dace da yankin don fuskantar ƙalubalen Arewa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Next Post: Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
Majalisun Najeriya Sun Amince Ta Karin Kasafin Kudi Afrika
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Ukraine Da Syria Zasuyi Haɗin Gwiwar Tsaro Labarai
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.