Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa
Published: December 9, 2025 at 7:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Gwamnonin jihohin arewa ta Naɗa Ezekiel Gomos a matsayin babban darakta don karfafa haɗin kan yankin

Kungiyar gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) ƙarƙashin jagorancin Shugabanta kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ta amince da naɗin Mista Ezekiel Gomos, OFR, a matsayin Babban daraktan sakatariyar ƙungiyar.

Naɗin dai ya yi daidai da sabbin alƙawuran da ƙungiyar ta ɗauka na ƙarfafa ayyukan hukumominta da inganta haɗin kai a tsakanin jihohin Arewa 19 wajen tinkarar ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

A cewar ƙungiyar, samar da ofishin Babban Daraktan wani kyakkyawan mataki ne na mayar da Sakatariyar ya zuwa cibiya mai inganci wajen haɗa kai da inganta manufofi, da aiki tare da kuma samar da tsare-tsaren ci gaba na dogon zango.

Mista Gomos, wadda tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Filato ne, ƙwararre ne a fannin tattalin arziƙi, siyasa da aikin gwamnati, da kuma inganta harkokin mulki, da bunƙasa kamfanoni masu zaman kansu da kuma ciyar da jama’a gaba.

Ƙwarewarsa ta haɗa da manyan ayyuka a manyan cibiyoyi masu tasiri irin su New Nigeria Development Company (NNDC) da kuma Hukumar Shirya Jarrabawa ta Yammacin Afirka (WAEC).

Bugu da ƙari, ya kasance ƙwararren mai bada shawara kuma shugaban tsangaya a Makarantar Kasuwanci ta Jos (JBS), makarantar data mayar da hankali wajen bunƙasa harkokin kasuwanci, horas da shugabanni da tsare-tsaren manufofi.

Mista Gomos ya shafe kusan shekaru ashirin yana aiki a Cibiyar Nazarin Siyasa da Dabaru ta Kasa (NIPSS) dake Kuru, inda ya bada gudummawa wajen horar da manyan shugabanni a faɗin Najeriya ta fuskar manufofi, dabaru da ci gaban ƙasa.

Sauran harkokin karatu na sabon Babban Daraktan sun haɗa da digiri na ɗaya dana biyu da ya yi a jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya da kuma Jami’ar East Anglia ta kasar Birtaniya.

Har ila yau mamba ne a wasu manyan cibiyoyi na duniya, ciki har da Hubert Humphrey Fellowship (na Jami’ar Minnesota) da Chevening Scholarship na Birtaniya da kuma kasancewarsa mamba a hukumar ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya (UNDP Fellowship) a Cibiyar Horaswa ta Ƙungiyar Ƙwadago ta Duniya (ILO) a Turin.

Gomos ya halarci manyan horaswar shugabanci a Makarantun Harvard Kennedy, da Jami’ar Chicago Booth School of Business, da Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Durham.

Da yake gabatar da takardar naɗin, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Mista Gomos ya yi amfani da ƙwarewarsa ta fannin jagoranci dabaru, ci gaban cibiyoyi da tsare-tsare don ƙarfafa sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin ta Arewa zuwa wata katafariyar dandalin haɗin gwiwar tsaro da tattalin arziƙin yankin da kuma ci gaba mai ɗorewa a faɗin Arewa.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewan ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa naɗin zai haifar da wani sabon yanayi na zurfafa haɗin gwiwa, da ingantaccen haɗin kai da kuma samar da matakan da suka dace da yankin don fuskantar ƙalubalen Arewa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Next Post: Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC

Karin Labarai Masu Alaka

Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
  • Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
  • Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.