Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
Published: December 12, 2025 at 11:05 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi EFCC da kauce wa ka’idar aikin ta na yaki da cin hanci, yana mai cewa hukumar ta koma “makamin siyasa” da ke farautar ’yan adawa.

A wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a Abuja, Atiku ya ce Siyasantar da binciken cin hanci ya lahanta kimar EFCC, yana mai zargin hukumar da zaben wadanda za ta bincika bisa siyasa, ba bisa hujjoji ba.

Ya ce kama tsohon Babban Lauyan Gwamnatin tarayya, Abubakar Malami (SAN), wani bangare ne na bin ’yan adawa cikin son zuciya, yana tuhumar EFCC da zama “reshen APC” da ke kokarin kafa tsarin jam’iyya ɗaya.

Atiku ya nuna cewa EFCC ta tsananta aiki ne bayan jam’iyyar ADC ta karu a matsayin babbar Jam’iyyar adawa, inda ya ambaci matakan da ya ce an dauka kan Malami da tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, yayin da ake watsi da zarge-zargen da suka shafi magoya bayan gwamnati.

Ya kuma zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da bai wa wasu tsoffin gwamnoni da ke da shari’o’in cin hanci mukaman gwamnati, yana cewa EFCC ta kasa nuna rashin amincewa.

Atiku ya yi ikirarin cewa da Malami ya koma APC, “da ba za a taba taba shi ba,” yana mai zargin hukumar da amfani da tsoratarwa don tilasta ’yan siyasa shiga jam’iyyar gwamnati.

Ya yi gargadi cewa ba za a samu ingantaccen yaki da cin hanci ba idan aka ci gaba da siyasantar da hukumomi, yana kira ga EFCC ta cire kanta daga tasirin siyasa domin kare mutuncin ta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
Next Post: Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna

Karin Labarai Masu Alaka

Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
  • Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya
  • Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.