Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko
Published: December 14, 2025 at 3:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jihar Gombe ta yi fice a gasar kiwon lafiya a Matakin farko ta ƙasa ta 2025, ta lashe Dalar Amurka 400,000

Jihar Gombe ta sake tabbatar da jajircewarta wajen inganta harkar kiwon lafiya, inda ta samu matsayi na biyu a shiyyar Arewa Maso Gabas a gasar Jagorancin Kiwon Lafiya Matakin Farko (PHC Leadership Challenge) ta shekarar 2025, tana yin fintinkau kan jihohi shida na shiyyar.

Sakamakon wannan ƙwazon da Gombe ta nuna wajen ƙarfafa tsarin kiwon lafiyar farko, an karrama ta da kyautar dala 400,000.

An miƙa kyautar ne yayin bikin karramawa na 2025 PHC Leadership Challenge da aka gudanar a cibiyar taro ta Bola Ahmed Tinubu, dake Abuja.

Bikin ya samu halartar manyan jami’ai da masu ruwa da tsaki a fannin lafiya, inda mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya jagoranci taron.

A shekarar da ta gabata ma, jihar Gombe ta kafa tarihi inda ta lashe PHC Leadership Challenge Innovation Award, lambar yabo ta kirkira da aka fara bayarwa tun bayan ƙaddamar da shirin, kuma ta zama ta biyu a Arewa Maso Gabas, lamarin da ya kawo mata kyautar dala $400,000.

Wannan ci gaba ya sake tabbatar da cewa Gombe na kan gaba wajen inganta harkar kiwon lafiya na asali a Najeriya.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC
Next Post: Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja Afrika
Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu Afrika
Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu Wasanni
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.