Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA
Published: December 16, 2025 at 7:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Attajirin dan kasuwa kuma Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Dakta Aliko Dangote, ya kai ƙara gaban Hukumar ICPC yana neman a binciki Manajan Darakta Hukumar sanya ido kan hada-hadar Albarkatun Man fetur (NMDPRA), Farouk Ahmed, bisa zargin cin hanci da rashawa da rayuwa sama da ƙarfin albashin ma’aikacin gwamnati.

Dangote ya yi zargin cewa Ahmed ya biya sama da dala miliyan 7 a matsayin kuɗin makaranta ga ‘ya’yansa huɗu a makarantu daban-daban a Switzerland, kuɗin da ya ce ba zai yiwu a samo shi daga dukkan albashinsa na aikin gwamnati ba.

A cikin ƙorafin, Dangote ya zargi shugaban NMDPRA da karkatar da kuɗaɗen gwamnati ta hanyar amfani da ofishinsa domin amfanin kansa, lamarin da ya ce ya cutar da ƙasar kuma ya jawo ce-ce-ku-ce a bainar jama’a.

Ya buƙaci ICPC ta binciki zargin tare da kamashi da gurfanar da Ahmed idan aka same shi da laifi, yana mai cewa a shirye yake ya gabatar da hujjoji idan aka gayyace shi.

Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro
Next Post: Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai

Karin Labarai Masu Alaka

Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
Afirka Ta Kudu Zata Fuskanci Koma Baya A Bangaren Samar Da Ayyukanyi Afrika
Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.