Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Published: December 17, 2025 at 3:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Donald Trump na Amurka ya kara wasu kasashe 7 cikin kasashen da gwamnatinsa zata haramta ma ‘yan kasar shiga kasar Amurka, cikinsu har da ‘yan Jamhuriyar Nijar.

Fadar White House ta fada ranar talata cewa, shugaba Trump ya sanya hannu a kan wata takardar sanarwa ta karawa da karfafa jerin kasashen da za a sanya ma al’ummarsu takunkumin shiga Amurka a saboda tabbatar da cewa ba su bincika ko bayar da bayanai ga hukumomin Amurka ta yadda zasu iya kare tsaron kasa daga irin wadannan mutane da zasu shigo kasa daga wadannan wurare.

Wannan matakin na ranar talata, a bayan haramta ma ‘yan Jamhuriyar Nijar shigowa Amurka, zai kuma kara da ‘yan kasashen Burkina Faso, Mali, Sudan ta Kudu, Sham ko Syria, da kuma wadanda suke rike da takardun tafiye-tafiye na hukumar mulkin Falasdinu.

Har ila yau wannan matakin yanzu ya haramta shigowar dukkan ‘yan kasashen Saliyo da Laos, wadanda a baya an takaita shigowarsu ne kawai.

Wannan sabon haramcin zai fara aiki daga ranar 1 ga wata mai zuwa na Janairu.

Sanya kasar Sham cikin jerin kasashen na zuwa ne duk da alkawarin da Trump yayi na cewa zai yi duk bakin kokarinsa na ganin kasar ta samu nasarar shawo kan matsalolinta a bayan tattaunawar da yayi da shugaban kasar, Ahmed al-Sharaa, wanda a can baya kwamanda ne na kungiyar al Qaida wanda Amurka ta taba sa takunkumi a kansa.

Fadar White House ta gabatar da hujjar cewa mutanen kasar Sham da suke shigowa Amurka suna ci gaba da zama har bayan karewar takardun bizar su, tana mai cewa dalilinta na daukar wannan matakin a kan Sham ke nan.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro
Next Post: Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai Amurka
‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Galatasaray Ta Yi Watsi Da Tayin €150m Daga Al-Hilal Kan Victor Osimhen Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.