Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Published: December 17, 2025 at 3:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Donald Trump na Amurka ya kara wasu kasashe 7 cikin kasashen da gwamnatinsa zata haramta ma ‘yan kasar shiga kasar Amurka, cikinsu har da ‘yan Jamhuriyar Nijar.

Fadar White House ta fada ranar talata cewa, shugaba Trump ya sanya hannu a kan wata takardar sanarwa ta karawa da karfafa jerin kasashen da za a sanya ma al’ummarsu takunkumin shiga Amurka a saboda tabbatar da cewa ba su bincika ko bayar da bayanai ga hukumomin Amurka ta yadda zasu iya kare tsaron kasa daga irin wadannan mutane da zasu shigo kasa daga wadannan wurare.

Wannan matakin na ranar talata, a bayan haramta ma ‘yan Jamhuriyar Nijar shigowa Amurka, zai kuma kara da ‘yan kasashen Burkina Faso, Mali, Sudan ta Kudu, Sham ko Syria, da kuma wadanda suke rike da takardun tafiye-tafiye na hukumar mulkin Falasdinu.

Har ila yau wannan matakin yanzu ya haramta shigowar dukkan ‘yan kasashen Saliyo da Laos, wadanda a baya an takaita shigowarsu ne kawai.

Wannan sabon haramcin zai fara aiki daga ranar 1 ga wata mai zuwa na Janairu.

Sanya kasar Sham cikin jerin kasashen na zuwa ne duk da alkawarin da Trump yayi na cewa zai yi duk bakin kokarinsa na ganin kasar ta samu nasarar shawo kan matsalolinta a bayan tattaunawar da yayi da shugaban kasar, Ahmed al-Sharaa, wanda a can baya kwamanda ne na kungiyar al Qaida wanda Amurka ta taba sa takunkumi a kansa.

Fadar White House ta gabatar da hujjar cewa mutanen kasar Sham da suke shigowa Amurka suna ci gaba da zama har bayan karewar takardun bizar su, tana mai cewa dalilinta na daukar wannan matakin a kan Sham ke nan.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro
Next Post: Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Shirin Ga Fili GA Doki Shirye-Shirye
  • Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.