Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa
Published: December 17, 2025 at 3:29 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 17, 2025

Tsohon kyaftin ɗin Super Eagles Ahmed Musa ya sanar da yin ritaya daga ƙwallon ƙafa ta ƙasa da ƙasa, wanda hakan ya kawo ƙarshen shekaru 15 da ya shafe yana wasa wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya.

Musa ya sanar da hakan ne a ranar Laraba ta shafin X ɗinsa a hukuma, yana mai bayyana shawarar tasa ta biyo bayan la’akari da ya yi sosai, ya ce sanya rigar kore da fari idan ya tuna abu ne mai ma’ana sosai a gare shi.

Na tuna lokacin da na fara tafiya ta ƙasa da ƙasa a matsayin matashin ɗan wasa, lokacin da aka gayyace ni zuwa ƙungiyoyin ƙasa na ‘yan ƙasa da shekaru 20, da 23 da manyan ƙungiyoyi, ban taba yin jinkirin zuwa Najeriya ba” in ji shi.

Musa ya ya buga wasanni 111 a ƙungiyar Super Eagles, wanda hakan ya sa ya zama ɗan wasa mafi buga wasa a tarihin ƙwallon ƙafa ta ƙasar.

Ya samu nasarar lashe gasar cin kofin ƙasashen Afirka ta 2013 kuma ya ci gaba da zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a Najeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, inda ya zura ƙwallaye masu kyau a kan Argentina a 2014 da Iceland a 2018.

Ya bayyana cimma wasanni 111 a matsayin babban abin farin ciki da girmamawa ne a koyaushe.

Musa ya ƙara da cewa lashe gasar AFCON ta 2013 wani muhimmin abu ne, zaman kyaftin ɗin ƙungiyar ya koya masa darussa masu mahimmanci game da shugabanci, haƙuri da kuma sanya wasu a gaba.

Babban Manaja kuma ɗan wasan ƙungiyar Kano Pillars ya gode wa abokan aikinsa, masu horarwa, da duk ma’aikatan da kuma masu kula da ƙwallon ƙafa saboda goyon bayan da suka ba shi na tsawon shekaru.

Ya kuma nuna matuƙar godiya ga magoya bayan Najeriya na gida da waje saboda alakar da sukayi da shi a tsawon aikinsa.

Ya kammala da cewa ya ba da dukkanin iyawarsa ga Najeriya kuma yana da kwarin gwiwa game da makomar Super Eagles, ya ƙara da cewa dangantakarsa da ƙasar za ta ci gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Next Post: Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu

Karin Labarai Masu Alaka

NFF Ta Nemi Afuwar Tinubu Da ’Yan Najeriya Kan Rashin Samun Tikitin Zuwa Gasar Kofin Duniya Ta Mata Wasanni
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23 Afrika
Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Osun: Adeleke Ya Doke Oyebamiji, Ya Ci Gaba Da Rike Kujerar Gwamna Afrika
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.