Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC, ta ayyana Gwamna Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Osun da aka gudanar ranar Asabar.
Adeleke, wanda ya samu damar yin wa’adi na biyu, ya doke babban abokin hamayyarsa, Bola Oyebamiji na jam’iyyar APC.
Jami’in tattara sakamakon zaɓen, Joshua Ogunwole, ne ya sanar da sakamakon a cibiyar tattara sakamakon INEC da ke Osogbo a safiyar Lahadi.
A cewarsa, Adeleke ya samu kuri’u 511,067, yayin da Bola Oyebamiji na APC ya samu 444,815, inda ya zo na biyu.
Najeem Salaam na jam’iyyar ADC ya zo na uku da kuri’u 17,180.


