Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari
Published: December 22, 2025 at 4:35 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 22, 2025

Hukumar NDLEA dake ayyukan hana sha da fataucin miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya tace tana tsananta bincike akan ‘yan matan nan guda biyu da ak damke yayin da sukayi yunkurin kai kwayar Tramadol ga wasu mutane dake tsare a gidan gyaran hali a Kano.

Jami’an hukumar kula da gidan gyaran halin ne suka damke ‘yan matan Maryam Ali ‘yar shekaru 19 da Hauwa Musa mai shekaru 20 a yayin binciken masu ziyarar daurarru a gidan gyaran hali na Goron Dutse a Kano.

Maryam Ali da Hauwa Musa sun boye kwayoyin tramadol din ne a cikin gurasa da sauran kayayyakin cimaka da suka dauko domin kaiwa samarin su dake daure.

DSP, Misbahu Lawan, kakakin hukumar kula da gyaran hali ta Najeriya shiyyar Kano yace damke ‘yan matan na daga cikin samakon tsauraran matakan da suke dauka akan masu ziyarar daurarru.

Yanzu haka dai hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya ta karbi ragamar gudanar da binciken kwakwaf akan wadannan ‘yan mata Maryam Ali da Hauwa Musa.

ASP, Sadiq Muhammad Maigatari, dake zaman kakakin hukumar ta NDLEA a Kano, yace Maryam Ali, guda cikin ‘yan Matan ta shaida musu cewa, tana shirin kaiwa saurayin ta kwayoyin tramadol da aka kamata dasu ne, wanda ke daure a can gidan gyran hali na Goron Dutse a Kano. Tace ita-ma tana amfani da nau’ikan kayayyakin san maye, irin su Codeine da tabar Wiwi.

Wannan yunkurin ‘yan mata domin safarar kwayoyi zuwa cikin gidajen da ake tsare da masu laifi, na kara fito da jan aikin dake gaban gwamnati da hukumominta wajen yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci
Next Post: Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.