Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari
Published: December 22, 2025 at 4:35 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 22, 2025

Hukumar NDLEA dake ayyukan hana sha da fataucin miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya tace tana tsananta bincike akan ‘yan matan nan guda biyu da ak damke yayin da sukayi yunkurin kai kwayar Tramadol ga wasu mutane dake tsare a gidan gyaran hali a Kano.

Jami’an hukumar kula da gidan gyaran halin ne suka damke ‘yan matan Maryam Ali ‘yar shekaru 19 da Hauwa Musa mai shekaru 20 a yayin binciken masu ziyarar daurarru a gidan gyaran hali na Goron Dutse a Kano.

Maryam Ali da Hauwa Musa sun boye kwayoyin tramadol din ne a cikin gurasa da sauran kayayyakin cimaka da suka dauko domin kaiwa samarin su dake daure.

DSP, Misbahu Lawan, kakakin hukumar kula da gyaran hali ta Najeriya shiyyar Kano yace damke ‘yan matan na daga cikin samakon tsauraran matakan da suke dauka akan masu ziyarar daurarru.

Yanzu haka dai hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya ta karbi ragamar gudanar da binciken kwakwaf akan wadannan ‘yan mata Maryam Ali da Hauwa Musa.

ASP, Sadiq Muhammad Maigatari, dake zaman kakakin hukumar ta NDLEA a Kano, yace Maryam Ali, guda cikin ‘yan Matan ta shaida musu cewa, tana shirin kaiwa saurayin ta kwayoyin tramadol da aka kamata dasu ne, wanda ke daure a can gidan gyran hali na Goron Dutse a Kano. Tace ita-ma tana amfani da nau’ikan kayayyakin san maye, irin su Codeine da tabar Wiwi.

Wannan yunkurin ‘yan mata domin safarar kwayoyi zuwa cikin gidajen da ake tsare da masu laifi, na kara fito da jan aikin dake gaban gwamnati da hukumominta wajen yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi da ababen sanya maye a Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci
Next Post: Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya Afrika
Borno: An Yi Kwanton Bauna Kan Ayarin Ɗan Takarar Gwamna Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki Afrika
Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
  • Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
  • Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
  • Gombe Ta Zo Ta Biyu Wajen Aiwatar Da Shirin L-PRES Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.