Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali
Published: December 23, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabanin kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso sun fara gudanar da taron kolin kungiyar AES a wannan litinin 22 ga watan disamban 2025 da nufin tattauna batutuwa da dama da suka shafi yankin da rayuwar al’umomin kasashen 3 masu fama da matsaloli iri daya musamman aika aikar kungiyoyin ta’addanci. wasu ‘yan Nijar suka fara bayyana fatansu kan wannan taro kamar yadda za a ji a wannan rahoto da wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana daga Yamai.

Janar Abdourahamane Tiani na Nijar da Keftin Ibrahim Traore na Burkina Faso da Assimi Goita na Mali shugaban rikon kungiyar AES a yayin zaman na wuni biyu za su yi bitar ayyukan hadin guiwar da suka gudanar a kungiyance kafin su tattauna kan batutuwan da zasu fi baiwa fifiko a nan gaba musamman ta inda za su bullowa lamarin tsaro, tattalin arziki aiyukan ci gaban jama’a diflomasiya da dai sauransu. shin ko ya ‘yan Nijar ke kallon wannan taro.?

Koda yake yanayin tsaro na kan gaban abubuwan da aka fi nuna damuwa kansu, ‘yan fafutika irinsu Hamidou Sidi Fody na kungiyar kulawa da Rayuwa na shawartar shugabanin kasashen 3 su kuma kara duba wata matsalar ta daban da ke dabaibaye harakokin tattalin arziki.

Nijar da Mali da Burkina Faso na cikin wata fafutikar tabbatar da ‘yancin kai a yayin da alamu ke nuna bayyanar babban sauyi a tafiyar siyasar duniya ta yau. abin da ke kara wa jama’ar yankin AES kwarin guiwa a game da manufofin da shugabanin kasashen 3 suka sa gaba sai dai akwai abin lura.

kungiyar AES ta samo asali a watan satumban 2023 kafin ta zama gamayya bayan watanni biyu da zumma duba alkibla guda a game da dukkan batutuwan da suka shafi tsaro diflomasiya tattalin arziki da sauransu, kasashen 3 sun fice daga CEDEAO a janerun 2024 saboda zargin kungiyar da zama ‘yar amshin shatan kasashen yammaci. sannan sun kori sojojin Faransa daga yankin sahel. daga bisani sun kafa rundunar hadin guiwa mai dakaru 5000 wace a karshen makon jiya aka kaddamar da aiyukanta a hukumance a ci gaba da jan damarar yaki da kungiyoyin ta’addanci.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi
Next Post: Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango

Karin Labarai Masu Alaka

Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
  • A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
  • Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.