Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin
Published: December 25, 2025 at 8:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Bam ya tashi cikin wani masallaci a lokacin sallar magariba jiya da daddare a wata kasuwa dake Maiduguri, babban birnin jihar Borno, inda ya kashe mutane akalla 5, ya raunata wasu fiye da 30.

‘Yan sanda sun ce watakila harin na kunar-bakin-wake ne, inda kakakin ‘yan sandan jihar, Nahum Daso ya fada cikin wata sanarwa cewa an samu abinda ya rage na wata rigar da ake zaton ta kunar bakin wake ce.

Wannan harin shine na baya bayan nan a yankin arewacin Najeriya, inda ake fama da ‘yan ta’addar Boko Haram da na ISWAP a yankin arewa maso gabashin kasar, da kuma kungiyoyin barayi da ‘yan fashin daji dake satar mutane suna garkuwa da su a yankin arewa maso yamma.

Babu wanda ya dauki alhakin kai harin ya zuwa yanzu, amma an fi alakanta harin kunar bakin wake da kungiyar Boko Haram.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi
Next Post: A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rikicin Siyasa A Jihar Rivers Sakamakon Ayyana Fubara A Matsayin Shugaban APC Siyasa
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
  • Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.