Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin
Published: December 25, 2025 at 8:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Bam ya tashi cikin wani masallaci a lokacin sallar magariba jiya da daddare a wata kasuwa dake Maiduguri, babban birnin jihar Borno, inda ya kashe mutane akalla 5, ya raunata wasu fiye da 30.

‘Yan sanda sun ce watakila harin na kunar-bakin-wake ne, inda kakakin ‘yan sandan jihar, Nahum Daso ya fada cikin wata sanarwa cewa an samu abinda ya rage na wata rigar da ake zaton ta kunar bakin wake ce.

Wannan harin shine na baya bayan nan a yankin arewacin Najeriya, inda ake fama da ‘yan ta’addar Boko Haram da na ISWAP a yankin arewa maso gabashin kasar, da kuma kungiyoyin barayi da ‘yan fashin daji dake satar mutane suna garkuwa da su a yankin arewa maso yamma.

Babu wanda ya dauki alhakin kai harin ya zuwa yanzu, amma an fi alakanta harin kunar bakin wake da kungiyar Boko Haram.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi
Next Post: A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
  • Sojojin Amurka Sunfara Isowa Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.