Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya
Published: December 26, 2025 at 5:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Trump ya ce Amurka ta kai “hare-hare masu yawa” masu kisa kan ‘yan ta’adda a Najeriya.

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ce a ranar Alhamis sojojin Amurka sun kai munanan hare-hare kan ‘yan ta’addar Daular Musulunci (ISIS) a Arewa maso Yammacin Najeriya, tare da yin barazanar ci gaba da kai hare-hare idan ‘yan ta’addan suka ci gaba da kashe kiristoci.

Shugaban ya bayyana hakan ne a shafinsa na X inda ya ƙara da cewa Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta aiwatar da hare-hare masu nasara da dama.

Ya rubuta cewa, “Yau da daddare, bisa umarni na a matsayi na na Babban Kwamandan Sojojin Amurka ta kaddamar da wani mummunan hari mai ƙarfi kan ‘yan ta’addar ISIS a Arewa maso Yammacin Najeriya, waɗanda suka dade suna kai hari tare da kashe Kiristoci marasa laifi.

“A baya na yi gargaɗi ga waɗannan ‘yan ta’adda cewa idan ba su daina kisan Kiristoci ba, za su fuskanci mummunan sakamako, kuma a daren yau hakan ta faru.

“Ma’aikatar Yaƙi ta aiwatar da hare-hare masu tsari da nagarta da dama, irin waɗanda Amurka kaɗai ke iya aiwatarwa.

“A ƙarƙashin jagoranci na, ƙasar mu ba za ta bari ta’addancin Musulunci mai tsatsauran ra’ayi ya bunƙasa ba.

“Allah Ya albarkaci sojojin mu, kuma Barka da kirsimeti ga kowa, har da ‘yan ta’addar da aka kashe, waɗanda za su ƙaru idan suka ci gaba da kisan Kiristoci.”

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
  • Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
  • Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Jam’iyyar ADC Ta Karbi Peter Obi Da Wasu Manyan ‘Yan-Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.