Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika

Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya
Published: December 26, 2025 at 5:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Trump ya ce Amurka ta kai “hare-hare masu yawa” masu kisa kan ‘yan ta’adda a Najeriya.

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ce a ranar Alhamis sojojin Amurka sun kai munanan hare-hare kan ‘yan ta’addar Daular Musulunci (ISIS) a Arewa maso Yammacin Najeriya, tare da yin barazanar ci gaba da kai hare-hare idan ‘yan ta’addan suka ci gaba da kashe kiristoci.

Shugaban ya bayyana hakan ne a shafinsa na X inda ya ƙara da cewa Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta aiwatar da hare-hare masu nasara da dama.

Ya rubuta cewa, “Yau da daddare, bisa umarni na a matsayi na na Babban Kwamandan Sojojin Amurka ta kaddamar da wani mummunan hari mai ƙarfi kan ‘yan ta’addar ISIS a Arewa maso Yammacin Najeriya, waɗanda suka dade suna kai hari tare da kashe Kiristoci marasa laifi.

“A baya na yi gargaɗi ga waɗannan ‘yan ta’adda cewa idan ba su daina kisan Kiristoci ba, za su fuskanci mummunan sakamako, kuma a daren yau hakan ta faru.

“Ma’aikatar Yaƙi ta aiwatar da hare-hare masu tsari da nagarta da dama, irin waɗanda Amurka kaɗai ke iya aiwatarwa.

“A ƙarƙashin jagoranci na, ƙasar mu ba za ta bari ta’addancin Musulunci mai tsatsauran ra’ayi ya bunƙasa ba.

“Allah Ya albarkaci sojojin mu, kuma Barka da kirsimeti ga kowa, har da ‘yan ta’addar da aka kashe, waɗanda za su ƙaru idan suka ci gaba da kisan Kiristoci.”

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.