Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya
Published: December 27, 2025 at 5:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Shugaban kasar Ukrain, Volodymr Zelensky yana so ya tattauna kan batutuwan da suka Shafi yankunan kasar da shugaban Amurka Donald Trump, wadanda su ne manyan abubuwa da suke kawo cikas wajen kawo karshen yakin ta da kasar Rasha.

Shugabannin biyu zasu tattauna ne a jihar Florida ranar Lahadi, a yayin da aka kusa karkare shirin zaman lafiya mai matakai ashirin, da kuma tabbatar da tsaro.

Da yake sanar wa da manema labarai kan batun tattaunawar, Zelensky ya ce za’a iya cimma matsaya da dama kafin zuwan sabuwar shekara, saboda fadar Washington ta zage dantse wajen ganin ta kawo karshen yaki gadan-gadan da Rasha ke yi da Ukrain, wanda ya kasance mafi muni a tarayyar turai tun bayan yakin duniya na biyu.

Israela ta kasance kasa ta farko da ta amince da Jamhuriyar Somaliland, da ta ayyana kan ta a matsayin kasa me cin gashin kan ta, ranar Jumu’a kuma wannan kuduri zai iya sauya fasalin dabi’un yankuna, kuma zai kawo kalubale ga ra’ayin Somalia na rashin son a warewa

Fira minista Benjamin Netanyahu, ya ce Israila zata nemi hadin guiwa da Somaliya a harkar noma, lafiya, fasaha da kuma tattalin arziki kuma a wani jawabi ya taya shugaban Somaliya Abdulrahman Muhammad Abdullahi murna, tare da yaba yadda yake gudanar da mulkin sa, ya kuma gayyace shi ya kai ziyara Israil.

Netanyahu ya ce wannan furuci, na daga cikin tsarin hadakar yankuna na Abraham Accords, wanda aka rattaba hannu a kai bisa ga shawara shugaba Donald Trump.

An kulla yarjejeniyar ne da aka tsara a shekarar 2020, lokacin mulkin Trump na farko, kuma ta kunshi kasar Isra’ila ta yi huldar diplomassiya bisa ka’ida da kasashen hadaddiyar daular larabawa, da Bahrain, tare da wasu kasashen da suka hadu daga baya.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda
Next Post: Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Jikkata Mutane A Arewacin Kasar Benin Afrika
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Zamu Tarwatsa Cibiyoyin Makamashi Da Cibiyoyin Mai Din Iran Amurka
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.