Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza
Published: December 29, 2025 at 10:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana samun karin kasashen dake fitowa suna yin Allah wadarai da amincewar da kasar Isra’ila ta yi da yankin Somaliland na kasar Somaliya a zaman kasa mai ‘yanci.

Ba a san dalilin da ya sa isra’ila ta fito ranar Jumma’a tana fadin cewa ta amince da Somaliland a zaman ‘yan tacciyar kasa ba, amma kuma a farkon shekarar nan jami’an Amurka da na Isra’ila sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa Isra’ila ta tuntubi jami’an yankin na Somaliland, a kan ko zasu karbi Falasdinawa na yankin Gaza, a wani bangare na shirin Shugaba Trump a wancan lokaci na sake tsugunar da mutanen Gaza a wani wuri kuma tuni dai Amurka ta yi watsi da wancan shirin nata.

Wata sanarwar hadin guiwar da kasashe fiye da 20 tare da kungiyar kasashen Musulmi ta duniya OIC suka bayar ta yi watsi da wannan amincewa da isra’ila ta ce ta yi da yankin na Somaliland a zaman kasa mai cin gashin kai, ganin irin yadda hakan zai yi mummunar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Yankin Somaliland ya bayyana ballewa daga Somaliya tun shekarar 1991, amma duk da cewa yana da gwamnati da takardar kudin sa daban, babu wata kasa a duniya da ta taba yarda da shi a zaman kasa.

Sanarwar kasashen ta kuma nuna rashin yarda ko miskala zarratin, da duk wani matakin da Isra’ila zata ce zata dauka dangane da wannan, wajen korar Falasdinawa karfi da yaji daga gidaje da garuruwa da yankunan su.

Ita ma kasar Sham, ko Syria, tayi tur da wannan mataki na Isra’ila a wata sanarwa dabam da ta bayar.

A ranar asabar, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da sanarwa tana jaddada ci gaba da mutunta kasar Somaliya wadda yankinta ya hada da yankin na Somaliland.

Gwamnatin tarayyar Somaliya ta fito ran jumma’a da kakkausar harshe tana yin tur da wannan matakin na Isra’ila da ta ce haramun ne.

Shi ma shugaban Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka, Mahmoud Ali Youssouf, yace duk wani matakin gurgunta diyaucin Somaliya na iya haddasa fitina a nahiyar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea
Next Post: Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Tunisiya Ya Tsawaita Dokar Da Baci A Kasar Labarai
Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
  • ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi Amurka
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
  • Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
  • Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.