Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza
Published: December 29, 2025 at 10:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana samun karin kasashen dake fitowa suna yin Allah wadarai da amincewar da kasar Isra’ila ta yi da yankin Somaliland na kasar Somaliya a zaman kasa mai ‘yanci.

Ba a san dalilin da ya sa isra’ila ta fito ranar Jumma’a tana fadin cewa ta amince da Somaliland a zaman ‘yan tacciyar kasa ba, amma kuma a farkon shekarar nan jami’an Amurka da na Isra’ila sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa Isra’ila ta tuntubi jami’an yankin na Somaliland, a kan ko zasu karbi Falasdinawa na yankin Gaza, a wani bangare na shirin Shugaba Trump a wancan lokaci na sake tsugunar da mutanen Gaza a wani wuri kuma tuni dai Amurka ta yi watsi da wancan shirin nata.

Wata sanarwar hadin guiwar da kasashe fiye da 20 tare da kungiyar kasashen Musulmi ta duniya OIC suka bayar ta yi watsi da wannan amincewa da isra’ila ta ce ta yi da yankin na Somaliland a zaman kasa mai cin gashin kai, ganin irin yadda hakan zai yi mummunar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Yankin Somaliland ya bayyana ballewa daga Somaliya tun shekarar 1991, amma duk da cewa yana da gwamnati da takardar kudin sa daban, babu wata kasa a duniya da ta taba yarda da shi a zaman kasa.

Sanarwar kasashen ta kuma nuna rashin yarda ko miskala zarratin, da duk wani matakin da Isra’ila zata ce zata dauka dangane da wannan, wajen korar Falasdinawa karfi da yaji daga gidaje da garuruwa da yankunan su.

Ita ma kasar Sham, ko Syria, tayi tur da wannan mataki na Isra’ila a wata sanarwa dabam da ta bayar.

A ranar asabar, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da sanarwa tana jaddada ci gaba da mutunta kasar Somaliya wadda yankinta ya hada da yankin na Somaliland.

Gwamnatin tarayyar Somaliya ta fito ran jumma’a da kakkausar harshe tana yin tur da wannan matakin na Isra’ila da ta ce haramun ne.

Shi ma shugaban Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka, Mahmoud Ali Youssouf, yace duk wani matakin gurgunta diyaucin Somaliya na iya haddasa fitina a nahiyar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea
Next Post: Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine

Karin Labarai Masu Alaka

An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika
  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona Wasanni
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.