Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa
Published: January 9, 2026 at 7:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kakakin majalisar dokokin jihar Rivers a Najeriya, Martins Amaewhule, ya zargi gwamna Siminalayi Fubara da tauye tafiyar dimokuraɗiyya a jihar.

Amaewhule ya yi wannan zargi ne a ranar Alhamis, jim kaɗan bayan majalisar ta fara shirin tsige gwamnan da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, bisa zargin aikata manyan laifuka.

A cewar kakakin, ɓangaren zartarwa na gwamnati ya kasa bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki sau da dama, musamman dangane da gabatar da kasafin kuɗi da amincewa da kashe kuɗaɗe.

“Babu wani abu da ke hana gwamnati gabatar da kasafin kuɗi da gangan ya zaɓi ƙin yin hakan,” in ji Amaewhule.

Ya ce gwamnan na faɗa wa magoya bayansa cewa wannan majalisa ba ta da wani ƙarfi, yana kiranta da “kare mara haƙora”, yana kuma cewa Majalisar Dokoki ta 10 ba za ta iya yin komai ko tilasta bin kundin tsarin mulki ba.

Amaewhule ya bayyana lamarin a matsayin mai haɗari ga dimokuraɗiyya a jihar Rivers.

“Wannan abin takaici ne ga dimokuraɗiyyarmu, Sir Siminalayi Fubara da Farfesa Ngozi Odu barazana ne ga dimokuraɗiyyarmu kuma idan aka bar su suka ci gaba da wannan hali, ina fargabar abin da zai faru da tafiyar dimokuraɗiyya a jihar Rivers,” in ji shi.

Ya kuma zargi gwamnan da mataimakiyarsa da kashe kuɗaɗen jama’a ba tare da amincewar Majalisa ba.

“Suna yawo daga wuri zuwa wuri suna kashe kuɗaɗen masu biyan haraji ba tare da amincewar majalisa ba,” in ji Amaewhule.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa
Next Post: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.