Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari
Published: January 13, 2026 at 4:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 13, 2026

Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cewa Najeriya za ta karɓi bakuncin taron Investopia tare da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a birnin Legas a watan Fabrairu mai zuwa, domin jawo hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a yayin taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na shekarar 2026, inda ya ce shirin zai taimaka wajen bunƙasa jarin da zai tallafa wa ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

A gefen taron, Najeriya da UAE sun kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar tattalin arziki ta CEPA, wadda ke da nufin zurfafa haɗin gwiwa a fannonin kasuwanci, makamashi, gine-gine, sufurin kayayyaki da kasuwancin zamani na intanet.

Shugaban UAE, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, tare da ministocin kasashen biyu, sun halarci sanya hannun kan yarjejeniyar da Tinubu ya bayyana a matsayin tarihi da dabarar bunkasa dangantakar kasashen biyu.

Tinubu ya bayyana cewa Investopia zai haɗa masu zuba jari, ‘yan kasuwa, masu kirkire-kirkire da masu tsara manufofi domin mayar da ra’ayoyi zuwa jarin da zai amfani al’umma, sannan ya ce Najeriya na da burin tara kusan dala biliyan 30 a duk shekara domin ayyukan sauyin yanayi da masana’antu masu kare muhalli, yana mai jaddada bukatar sauya tsarin hada-hadar kuɗin duniya domin sauƙaƙa wa ƙasashe masu tasowa samun jari ba tare da nauyin bashi ba.

Shugaban ƙasar ya kuma yi nuni da gyare-gyaren makamashi da tattalin arziki da gwamnatinsa ke aiwatarwa, ciki har da Dokar Lantarki ta 2023 da kuma manufofin kasuwar carbon, yana cewa hakan ya ƙara amincewar masu zuba jari.

Ya ƙara da cewa fitar da kayayyakin da ba na mai ba ya ƙaru da kashi 21 cikin 100, tare da alkawarin cewa Najeriya a shirye take ta yi aiki da abokan hulɗa domin gina ci gaba mai ɗorewa, adalci da amfani ga kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci
Next Post: Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
  • Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
  • Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa Labarai
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.