Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC
Published: January 14, 2026 at 9:17 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kaddamar da shirin rajistar mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta hanyar zamani a jihar Gombe, karkashin jagorancin Gwamnan jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Da yake kaddamar da shirin, Gwamna Inuwa Yahaya ya bukaci daukacin mambobin jam’iyyar da su koma mazabunsu domin yin rajistar yadda ya kamata ya kuma jaddada cewa mallakar Katin Zabe na Dindindin (PVC) da Katin Shaidar Dan Kasa (NIN) su ne muhimman sharuɗɗan samun cikakken rajista a jam’iyyar.

Gwamnan ya kuma yaba da irin namijin kokarin da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ke yi wajen ci gaban kasa da kuma karfafa matsayi da farin jinin jam’iyyar APC.

A nasa bangaren, Shugaban jam’iyyar APC na jihar Gombe, Nitte Amangal, ya tabbatar da cewa aikin rajistar zai gudana a dukkan mazabu 114 da ke fadin jihar, tare da bukatar mambobi su yi rajista a inda suka fito.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu
Next Post: Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas

Karin Labarai Masu Alaka

Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu Siyasa
Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Miyetti Allah Ta Bukaci Mambobinta Su Marawa Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna Baya A Gombe Afrika
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.