Yau a ke cika shekaru 60 da yin kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto a juyin mulkin soja na farko a Najeriya.
Wasu hafsoshin soja daga akasari kabilar Igbo ne su ka aiwatar da juyin mulkin ranar 15 ga Janairu 1966.
Shi dai wannan juyin mulkin da ya haddasa zubar da jini ya yi sanadiyyar kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello, Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyan kudu maso yamma Chief Ladoke Akintola a birnin Badun.
Juyin mulkin ya shafi manyan ‘yan siyasar Arewa da kuma Chief Akintola na Yarbawa amma bai taba kabilar Igbo ba.
Chukwuma Nzeogwu wanda hafsan soja ne da ya ci alfarmar Sardauna shi ya shiga gidan Firimiya ya yi ma sa kisan gilla shi da matarsa Hafsa da ta yi kokarin tare albarushi.
Nzeogwu ya nuna farin ciki da kisan da kuma mubaya’arsa ga Janar Johnson Aguiyi Ironsi wanda ya haye madafun iko a wannan yanayi na zubar da jini.
An tabbatar kalaman Sir Ahmadu Bello kan shirin ba wa al’ummar Arewa fifiko su amshi guraben ayyukan lardinsu da kaucewa babakeren Igbo ya zama daga dalilan kisan.
Dattijon NEPU da ta yi adawa da jam’iyyar NPC ta Sardauna Alhaji Hussaini Gariko ya ce adalcin Sardauna da amanarsa ababen koyi ne ga dukkan jagororin al’ummarmu.
Bayan kisan gilla Sardauna da Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa, Janar Johnson Aguiyi Ironsi ya hau karaga amma kimanin wata 6 da kwana 15 a ka kifar de gwamnatinsa kuma har daga bisani ya kai ga yakin basasar Najeriya yayin da gwamnan Soja na jihar kudu maso gabar Odumegwu Ojukwu ya ayyana ballewa daga Najeriya.
Dakarun gwamnatin tarayya sun fafata tun daga 1967-1970 har su ka yi nasarar sake hade kasar.
Har yanzu Najeriya ba ta warware daga fitinar juyin mulkin 1966 ba.


