Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato
Published: January 15, 2026 at 8:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: January 15, 2026

Yau a ke cika shekaru 60 da yin kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto a juyin mulkin soja na farko a Najeriya.

Wasu hafsoshin soja daga akasari kabilar Igbo ne su ka aiwatar da juyin mulkin ranar 15 ga Janairu 1966.

Shi dai wannan juyin mulkin da ya haddasa zubar da jini ya yi sanadiyyar kisan gilla ga Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello, Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa da Firimiyan kudu maso yamma Chief Ladoke Akintola a birnin Badun.

Juyin mulkin ya shafi manyan ‘yan siyasar Arewa da kuma Chief Akintola na Yarbawa amma bai taba kabilar Igbo ba.

Chukwuma Nzeogwu wanda hafsan soja ne da ya ci alfarmar Sardauna shi ya shiga gidan Firimiya ya yi ma sa kisan gilla shi da matarsa Hafsa da ta yi kokarin tare albarushi.

Nzeogwu ya nuna farin ciki da kisan da kuma mubaya’arsa ga Janar Johnson Aguiyi Ironsi wanda ya haye madafun iko a wannan yanayi na zubar da jini.

An tabbatar kalaman Sir Ahmadu Bello kan shirin ba wa al’ummar Arewa fifiko su amshi guraben ayyukan lardinsu da kaucewa babakeren Igbo ya zama daga dalilan kisan.

Dattijon NEPU da ta yi adawa da jam’iyyar NPC ta Sardauna Alhaji Hussaini Gariko ya ce adalcin Sardauna da amanarsa ababen koyi ne ga dukkan jagororin al’ummarmu.

Bayan kisan gilla Sardauna da Firaministan Najeriya Sir Abubakar Tafawa Balewa, Janar Johnson Aguiyi Ironsi ya hau karaga amma kimanin wata 6 da kwana 15 a ka kifar de gwamnatinsa kuma har daga bisani ya kai ga yakin basasar Najeriya yayin da gwamnan Soja na jihar kudu maso gabar Odumegwu Ojukwu ya ayyana ballewa daga Najeriya.

Dakarun gwamnatin tarayya sun fafata tun daga 1967-1970 har su ka yi nasarar sake hade kasar.

Har yanzu Najeriya ba ta warware daga fitinar juyin mulkin 1966 ba.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AS-SARDAUNAS-ASSASSAINATION-CLOCKS-60-YEARS.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Next Post: Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.