Hukumomi a Afirka ta Kudu sun ce ruwan sama me karfi da ambaliyar ruwa ya yi sanadiyar rayukan mutane fiye da dari a kasashen Afirka ta Kudu, Mozambique, da Zimbabwe a makonnin nan, kuma sun yi gargadin sake samun mummunan yanayi a fadin yankin na kudancin Afirka.
Jiragen sojoji masu saukar ungulu sun kubutar da mutane da suka fake a saman gidaje, yayin da ake ceto daruruwan ‘yan yawon bude ido daga wani babban wurin aje namun daji da yake daya daga cikin mafi girma a duniya.
Kasar Mozambique ce ta fi shan bugu, inda aka samu ambaliyar ruwa da ya ratsa yankunan ta na tsakiya da Lardukan da ke kudancin kasar kuma ma’aikatar lura da lalacewar yanayi da rage hadurra ta kasar ta ce mutane 103 ne suka rasa rayukan su sakamakon yanayi na ruwan sama me karfi tun shekarar da ta gabata, duk da mutuwar ta kunshi wasu dalilai da ban da ya hada da fadowar aradu, fadowar gine-gine, da nutsewa a ruwa sakamakon ambaliya.
Abin ya Shafi fiye da mutane 200,000 a Mozambique, dubbanan gidaje sun lalace ba zasu zaunu ba, a kasar da talauci ya riga ya yi katutu, ga karancin ababen more rayuwa, da ta sha fuskantar iskar guguwa mai karfi da aikata barna a cewar hukumar shirin samar da abinci ta duniya.


