Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain
Published: January 19, 2026 at 8:58 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani jirgin kasa mai saurin tafiya ya goce daga kan layin dogonsa ya kara tare da ture wani jirgin daban daga kan layinsa na dogo a yankin kudancin Spain, inda hukumomin ‘yan sanda suka tabbatar da cewa mutane akalla 21 sun mutu.

Wannan hatsarin ya faru ne a kusa da Adamuz a lardin Cordoba, inda gidan telebijin na kasar, Television Espanola, ya kara da cewa mutane 100 sun ji rauni, guda 25 daga cikinsu mummunan rauni.

Gidan telebijin na Espanola ya kara da cewa direban daya daga cikin jiragen wanda ya taso daga Madrid a kan hanyar zuwa Huelva, na daga cikin wadanda suka mutu.

Kamfanin dake tafiyar da layukan dogo na kasar, Adif, ya fada a wata sanarwar da ya bayar ta shafin sada zumunci cewa jirgin da ya fito daga Malaga a kan hanyar zuwa Madrid shine ya fara kauce ma layin dogonsa a Adamuz, ya fada kan daya layin dogon, ya kara da jirgin da ya taso daga Madrid a kan hanyar zuwa Huelva.

Kamfanin Adif yace hatsarin ya faru da karfe 6:40 na maraicen kasar, kimanin minti 10 bayan da jirgin farko ya bar Cordoba ya doshi Madrid.

Kamfanin Iryo, wanda ya mallaki jirgin kasan ya bayyana jimami da mummunan takaicin abinda ya faru, ya kuma kaddamar da shirinsa na gaggawa da yin aiki tare da hukumomin da abin ya shafa wajen tinkarar wannan lamari.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025.
Next Post: An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya

Karin Labarai Masu Alaka

Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus
  • Hukumar ‘Yan Sanda Sun Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe
  • Kasar Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Biri
  • Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kwango
  • Kungiyoyi Sunyi Kasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.