Shugabannin kasashen turai da take-taken shugaban Amurka Donald Trump ta girgiza su, suna kokarin nuna hadin kai a taron shekara shekara kan tattalin arziki da harkokin duniya a Davos na kasar Switzeland, a dai dai lokacin da manyan ‘yan kasuwa a turai suke gargadin kada a biye wa zuciya wajen maida martani kan burin shugaba Trump game da tsibirin Greenland.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron, yace kada turai ta amince da “rayuwa ta mai karfi,” yace abun takaici ne wai har turai tana jan kafa wajen amfani da “dokar hana tursasawa” kan Amurka.
Mun yarda muna bukatar habaka tattalin arziki, muna bukatar daidaituwar al’amura a duniyan nan, amma muna bukatar mutunci, ba biyayya ga ‘yan cin-zali-ba.” Macron ya fadawa taron na shekara shekara, kwana daya kamin zuwan shugaban Amurka Donald Trump a zauren taron.
Ba tare da ta ambaci sunan Trump kai tsaye ba, shugabar hukumar tarayyar turai, Ursula Von der Leyen, ta bayyana bukatar tarayyar turai ta maida martani kan canji cikin gaggawa da yake wakana a duniya, tana mai cewa, lamarin yasa turai tayi ittifaki na zama mai ‘yancin kai.
“Lokaci yayi da zamu yi amfani da wannan dama, wajen gina turai mai cin gashin kai,” Vonder Leyen ta fada a cikin jawabinta.
PM Belgium, Bart De Wever, yace lokaci yayi da kungiyar tarayyar turai mai wakilai 27, zata hada kai ta gayawa shugaba Trump yana neman wuce gona da iri. Ko mu hada kai mu tsira tare, ko kuma mu ci gaba da zama a wargaje, Wever ya fada a wata tattaunawa da aka yi a wajen taron da ake yi a Davos.


