Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki
Published: January 20, 2026 at 9:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabannin kasashen turai da take-taken shugaban Amurka Donald Trump ta girgiza su, suna kokarin nuna hadin kai a taron shekara shekara kan tattalin arziki da harkokin duniya a Davos na kasar Switzeland, a dai dai lokacin da manyan ‘yan kasuwa a turai suke gargadin kada a biye wa zuciya wajen maida martani kan burin shugaba Trump game da tsibirin Greenland.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron, yace kada turai ta amince da “rayuwa ta mai karfi,” yace abun takaici ne wai har turai tana jan kafa wajen amfani da “dokar hana tursasawa” kan Amurka.

Mun yarda muna bukatar habaka tattalin arziki, muna bukatar daidaituwar al’amura a duniyan nan, amma muna bukatar mutunci, ba biyayya ga ‘yan cin-zali-ba.” Macron ya fadawa taron na shekara shekara, kwana daya kamin zuwan shugaban Amurka Donald Trump a zauren taron.

Ba tare da ta ambaci sunan Trump kai tsaye ba, shugabar hukumar tarayyar turai, Ursula Von der Leyen, ta bayyana bukatar tarayyar turai ta maida martani kan canji cikin gaggawa da yake wakana a duniya, tana mai cewa, lamarin yasa turai tayi ittifaki na zama mai ‘yancin kai.

“Lokaci yayi da zamu yi amfani da wannan dama, wajen gina turai mai cin gashin kai,” Vonder Leyen ta fada a cikin jawabinta.

PM Belgium, Bart De Wever, yace lokaci yayi da kungiyar tarayyar turai mai wakilai 27, zata hada kai ta gayawa shugaba Trump yana neman wuce gona da iri. Ko mu hada kai mu tsira tare, ko kuma mu ci gaba da zama a wargaje, Wever ya fada a wata tattaunawa da aka yi a wajen taron da ake yi a Davos.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana
Next Post: Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki Afrika
  • Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.