Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno
Published: January 22, 2026 at 8:06 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu majiyoyin tsaro a Najeriya sun ce an kashe sojoji akalla 8, aka raunata wasu 50 a lokacin da ‘yan ta’addan kungiyar Boko Haram suka kai farmaki a kan wani sansanin sojoji dake jihar Borno.

Majiyoyin suka ce ‘yan bindigar na Boko Haram sun isa a kan babura da motoci masu sulke a ranar litinin.

Wata majiyar soja a Najeriya ta fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan sansani an kafa shi ne a wani bangare na farmakin da ake kaiwa da nufin tumbuke ‘yan Boko Haram daga wani yankin da suka lakaba ma suna Timbuktu, wanda yanki ne da ya tashi daga Damboa zuwa Maiduguri, ya yi yamma zuwa Ngamdu, ya sake yin gabas zuwa Damboa.

A wata sanarwar da ta bayar ranar laraba, rundunar sojojin Najeriya ta ce sojoji sun kori ‘yan Boko Haram daga sansanoninsu da dama dake cikin wannan yanki na Timbuktu, suka kuma wargaza shirye-shiryen kai hare-hare da motocin da aka dana bama-bamai cikinsu.

Rundunar ta ce dakaru sun samu nasarar katse hanzarin wata motar da aka shake ta bama-bamai, amma wata a bayanta ta samu halin shigewa cikin inda sojojin suka yi daga ta kashe wasu sojoji da fararen hula masu aikin sa kai, wadanda aka fi sani da suna Civilian-JTF.

Wani dan rundunar Civilian-JTF ya tabbatar da wannan fada da aka gwabza yana mai fadin cewa ‘yan Boko Haram da suka kai harin sun ninka sojojin dake sansanin.

Tuni dai rundunar sojojin ta janye wadannan sojoji zuwa babban sansaninta dake garin Damboa kuma an kwashi gawarwakin wadanda suka mutu da wadanda suka ji rauni zuwa asibitin sojojin dake barikin Maimalari a garin Maiduguri.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Next Post: Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
Sojin Saman Najeriya Sun Lalata Sansanonin ‘Yan Ta’adda Afrika
Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai Amurka
An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
  • Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.