Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno
Published: January 22, 2026 at 8:06 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu majiyoyin tsaro a Najeriya sun ce an kashe sojoji akalla 8, aka raunata wasu 50 a lokacin da ‘yan ta’addan kungiyar Boko Haram suka kai farmaki a kan wani sansanin sojoji dake jihar Borno.

Majiyoyin suka ce ‘yan bindigar na Boko Haram sun isa a kan babura da motoci masu sulke a ranar litinin.

Wata majiyar soja a Najeriya ta fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa wannan sansani an kafa shi ne a wani bangare na farmakin da ake kaiwa da nufin tumbuke ‘yan Boko Haram daga wani yankin da suka lakaba ma suna Timbuktu, wanda yanki ne da ya tashi daga Damboa zuwa Maiduguri, ya yi yamma zuwa Ngamdu, ya sake yin gabas zuwa Damboa.

A wata sanarwar da ta bayar ranar laraba, rundunar sojojin Najeriya ta ce sojoji sun kori ‘yan Boko Haram daga sansanoninsu da dama dake cikin wannan yanki na Timbuktu, suka kuma wargaza shirye-shiryen kai hare-hare da motocin da aka dana bama-bamai cikinsu.

Rundunar ta ce dakaru sun samu nasarar katse hanzarin wata motar da aka shake ta bama-bamai, amma wata a bayanta ta samu halin shigewa cikin inda sojojin suka yi daga ta kashe wasu sojoji da fararen hula masu aikin sa kai, wadanda aka fi sani da suna Civilian-JTF.

Wani dan rundunar Civilian-JTF ya tabbatar da wannan fada da aka gwabza yana mai fadin cewa ‘yan Boko Haram da suka kai harin sun ninka sojojin dake sansanin.

Tuni dai rundunar sojojin ta janye wadannan sojoji zuwa babban sansaninta dake garin Damboa kuma an kwashi gawarwakin wadanda suka mutu da wadanda suka ji rauni zuwa asibitin sojojin dake barikin Maimalari a garin Maiduguri.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Next Post: Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
  • Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.