A Sudan mayakan RSF ko Rapid Support Forces da turanci sun zafafa kai hare hare da jiragen yakin da babu matuka da ake kira Drones da turance a ciki da kewayen birnin al-obeid da ke tsakiyar Sudan, a yayinda yakin basasar yake kara kusa da birnin da yake karkashin sojoji, wadda ya haddasa hasarar rayuka farar hula masu yawa, a lokuta daban daban har sau biyu, kamar yadda mazauna birnin suka fada.

Birnin yana da muhimmancin gaske, kuma shine babban birnin jihar Kordofan, birni da ya raba yankin na Kordofan da yankin Darfur dake hanun ‘yan tawaye, da kuma gabashin kasar dake hanun sojojin Sudan.
Rahotanni suka ce bayan da ‘yan tawayen na RSF suka kama yammacin yankin Darfur cikin watan Oktoba, yanzu sun maida hankalin su yankin kordofan, kuma a duk mako sai sun kai hari a da jiragen Drones, kamar yadda mazauna yankin suka fada.
Zuwa yanzu dakarun na RSF basu tunkari al-obeid kai tsaye ba, inda jama’a suke ci gaba da harkokin su na yau da kullum duk da barazanar suke hangowa.
Sojojin Sudan da masu mara musu baya, sun kama wuri bayan birnin na a-Obeid.
A halinda ake ciki kuma, wata kungiyar tallafawa yara da ake kira Save the Children da turanci, tace fiye da yara miliyan 8 ne da suka kai shekarun Shiga makaranta da a halin yanzu basa karatu, sakamakon yakin basasar da kasar take famada shi.


