Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya gargadi sarakunan gargajiya da su daina raba filaye ba bisa ka’ida ba, inda ya ce duk wanda aka kama yana aikata hakan zai Rasa kujerar sa.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin ziyararsa ga Elulu na Mopa, Oba Muyiwa Ibeun, a fadarsa, ya rawaito cewa gwamnan ya kuma duba ayyukan gine-gine da ake ci gaba da yi a yankin.
Sarkin gargajiyar, yayin karɓar gwamnan, ya yabawa kokarin da gwamnatin ke yi wajen bunƙasa jihar, tare da nuna godiyarsa bisa gina titunan Mopa township da gwamnatocin baya suka bari ba’a kammalaba
Oba Ibeun ya sake jaddada goyon bayan masarautar da al’ummar Mopa ga gwamnati, inda ya bayyana cewa masarautar ta shahara da zaman lafiya. Ya kuma yabawa gwamnan kan dabarun tsaro da ya kafa, yana mai cewa abin koyi ne wajen kare jihar.
A nasa jawabin, Gwamna Ahmed Usman Ododo ya gode wa Oba Ibeun bisa kiyaye zaman lafiya da haɗin Kai.


