Tsagin jam’iyyar APC a jihar Rivers karkashin jagorancin Emeka Beke ya yi maraba da tabbacin da Shugaba Bola Tinubu ya bayar na amincewa da Gwamna Siminalayi Fubara a matsayin jagoran jam’iyyar APC a jihar.
Sun bayyana hakan a matsayin hujja da ta tabbatar da matsayinsu da suka daɗe suna a kai, duk da rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyar.
A cikin wata sanarwa ga manema labarai da aka fitar ranar Juma’a, wadda kakakin ɓangaren jam’iyyar, Darlington Nwauju, ya sanya wa hannu, jam’iyyar ta ce wannan tabbaci da aka isar ta hannun mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin sadarwar manufofi, Daniel Bwala, ya nuna jajircewar shugaba Tinubu wajen bin kundin tsarin jam’iyyar APC da kuma ka’idojin jam’iyyar da aka kafa tun da daɗewa.


