Ranar Alhamis a London, Britaniya ta gurfabar da wasu jami’an Immigration su biyar gaban kotu kan zargin rashin da’a a bakin aiki, da hada baki ko makarkashiyar yi wa ‘yan gudun hijira sata, wadanda suka isa kasar cikin kananan kwale-kale ko jiragen ruwa.
Mutanen John Bernthal dan shekaru 53 da haifuwa, da Ben Edwards, dan shekaru 45, da Lee Ann Evans dan shekaru 42 da wasun su mutane biyu, duk ana tuhumar su da yiwa ‘yan gudun hijira sata, tsakanin watan Agustan 2021-zuwa watan Nuwamban shekara ta 2022. Ana tuhumar ko wanne daga cikin su da laifi daya na rashin da’a a bakin aiki, da kuma laifi daya na halatta kudaden haram.
An bada belin su kamun zaman ci gaba da sauraron shari’ar a cikin watan Feburairu mai zuwa.


