Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango
Published: February 3, 2026 at 9:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD a Kwango, zata tura tawagarta ta farko da zata sa ido kan tsagaita wuta tsakanin gwamnatin Kwango da kungiyar ‘yan tawayen kasar da ake kira da lakabin AFC/M23. Ma’aikatar ta bayyana haka ne ranar Litinin, bayan da ta jagoranci zaman shawarwari a Doha.

Qatar tace tawagar ta MDD zata girke ne a Uvira wani wuri mai muhimmanci a gabashin Kwango, da ‘yan tawayen kasar suka kama cikin watan Disamba bara, lokacin da suka danno kamar guguwa suna ta kama wurare, birni da dakarun kasar ta Kwango suka sake shiga da cikin watan jiya bayanda ‘yan tawayen suka ce za su janye.

Sanarwar da Qatar ta bayar a daren ranar litinin, alama ce ta ana samun ci gaba a shawarwarin da Doha take shiga tsakani ana gudanarwa tsakanin Kwangon da ‘yan tawayen na M23, wadanda a bara suka kama kasa da bata taba rikewa ba gabashin Kwango.

A gefe daya kuma Amurka tana shiga tsakani a wani zaman shawarwari tsakanin Kwangon, da kuma Rwanda, wacce MDD da manyan kasashen yammacin duniya suka ce itace uwargijiyar M23, zargi da hukumomin kasar a Kigali suka musanta.

Yunkuri na baya bayan na farfado da shirin sa ido kan yarjejeniyar tsagaita wutan ya biyo bayan ci gaba da gwabza fada a gabashin Kwangon.

Ahalinda a ke ciki kuma, kudin inshora na gudanar da harkokin kasuwanci a Kwangon ya tashi ninkin ba-ninkin, kamar yadda masu aikin sayar da inshora suka gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa
Next Post: Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
Anyi Asarar Biliyoyin Naira A Gobarar Kasuwar Singa Labarai
Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
  • Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
  • Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.