Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango
Published: February 3, 2026 at 9:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD a Kwango, zata tura tawagarta ta farko da zata sa ido kan tsagaita wuta tsakanin gwamnatin Kwango da kungiyar ‘yan tawayen kasar da ake kira da lakabin AFC/M23. Ma’aikatar ta bayyana haka ne ranar Litinin, bayan da ta jagoranci zaman shawarwari a Doha.

Qatar tace tawagar ta MDD zata girke ne a Uvira wani wuri mai muhimmanci a gabashin Kwango, da ‘yan tawayen kasar suka kama cikin watan Disamba bara, lokacin da suka danno kamar guguwa suna ta kama wurare, birni da dakarun kasar ta Kwango suka sake shiga da cikin watan jiya bayanda ‘yan tawayen suka ce za su janye.

Sanarwar da Qatar ta bayar a daren ranar litinin, alama ce ta ana samun ci gaba a shawarwarin da Doha take shiga tsakani ana gudanarwa tsakanin Kwangon da ‘yan tawayen na M23, wadanda a bara suka kama kasa da bata taba rikewa ba gabashin Kwango.

A gefe daya kuma Amurka tana shiga tsakani a wani zaman shawarwari tsakanin Kwangon, da kuma Rwanda, wacce MDD da manyan kasashen yammacin duniya suka ce itace uwargijiyar M23, zargi da hukumomin kasar a Kigali suka musanta.

Yunkuri na baya bayan na farfado da shirin sa ido kan yarjejeniyar tsagaita wutan ya biyo bayan ci gaba da gwabza fada a gabashin Kwangon.

Ahalinda a ke ciki kuma, kudin inshora na gudanar da harkokin kasuwanci a Kwangon ya tashi ninkin ba-ninkin, kamar yadda masu aikin sayar da inshora suka gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa
Next Post: Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
Chadi Ta Sauyawa ‘Yan Gudun Hijira Matsuguni Afrika
Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika
Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya Afrika
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • ‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.