Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD a Kwango, zata tura tawagarta ta farko da zata sa ido kan tsagaita wuta tsakanin gwamnatin Kwango da kungiyar ‘yan tawayen kasar da ake kira da lakabin AFC/M23. Ma’aikatar ta bayyana haka ne ranar Litinin, bayan da ta jagoranci zaman shawarwari a Doha.
Qatar tace tawagar ta MDD zata girke ne a Uvira wani wuri mai muhimmanci a gabashin Kwango, da ‘yan tawayen kasar suka kama cikin watan Disamba bara, lokacin da suka danno kamar guguwa suna ta kama wurare, birni da dakarun kasar ta Kwango suka sake shiga da cikin watan jiya bayanda ‘yan tawayen suka ce za su janye.
Sanarwar da Qatar ta bayar a daren ranar litinin, alama ce ta ana samun ci gaba a shawarwarin da Doha take shiga tsakani ana gudanarwa tsakanin Kwangon da ‘yan tawayen na M23, wadanda a bara suka kama kasa da bata taba rikewa ba gabashin Kwango.
A gefe daya kuma Amurka tana shiga tsakani a wani zaman shawarwari tsakanin Kwangon, da kuma Rwanda, wacce MDD da manyan kasashen yammacin duniya suka ce itace uwargijiyar M23, zargi da hukumomin kasar a Kigali suka musanta.
Yunkuri na baya bayan na farfado da shirin sa ido kan yarjejeniyar tsagaita wutan ya biyo bayan ci gaba da gwabza fada a gabashin Kwangon.
Ahalinda a ke ciki kuma, kudin inshora na gudanar da harkokin kasuwanci a Kwangon ya tashi ninkin ba-ninkin, kamar yadda masu aikin sayar da inshora suka gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.


