Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika

Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango
Published: February 3, 2026 at 9:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD a Kwango, zata tura tawagarta ta farko da zata sa ido kan tsagaita wuta tsakanin gwamnatin Kwango da kungiyar ‘yan tawayen kasar da ake kira da lakabin AFC/M23. Ma’aikatar ta bayyana haka ne ranar Litinin, bayan da ta jagoranci zaman shawarwari a Doha.

Qatar tace tawagar ta MDD zata girke ne a Uvira wani wuri mai muhimmanci a gabashin Kwango, da ‘yan tawayen kasar suka kama cikin watan Disamba bara, lokacin da suka danno kamar guguwa suna ta kama wurare, birni da dakarun kasar ta Kwango suka sake shiga da cikin watan jiya bayanda ‘yan tawayen suka ce za su janye.

Sanarwar da Qatar ta bayar a daren ranar litinin, alama ce ta ana samun ci gaba a shawarwarin da Doha take shiga tsakani ana gudanarwa tsakanin Kwangon da ‘yan tawayen na M23, wadanda a bara suka kama kasa da bata taba rikewa ba gabashin Kwango.

A gefe daya kuma Amurka tana shiga tsakani a wani zaman shawarwari tsakanin Kwangon, da kuma Rwanda, wacce MDD da manyan kasashen yammacin duniya suka ce itace uwargijiyar M23, zargi da hukumomin kasar a Kigali suka musanta.

Yunkuri na baya bayan na farfado da shirin sa ido kan yarjejeniyar tsagaita wutan ya biyo bayan ci gaba da gwabza fada a gabashin Kwangon.

Ahalinda a ke ciki kuma, kudin inshora na gudanar da harkokin kasuwanci a Kwangon ya tashi ninkin ba-ninkin, kamar yadda masu aikin sayar da inshora suka gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa
Next Post: Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona
  • Kocin Newcastle Matthias Ya Ce Lewis Hall Ba Zai Koma Manchester United Ba
  • Dan Wasan Baya Na Chelsea, Disasi, Zai Yi Gwajin Lafiyarsa A Crystal Palace
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya Afrika
  • Liverpool Tayi Rashin Nasara A Wasanni Tara Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.