Shugaban Amurka Donald Trump ya fada ranar laraba cewa, basu cimma takamammen matsaya ba da PM Isra’ila Benjamin Netanyahu bayan shawarwari da suka yi game da lamarin Iran, duk da haka yace Amurka zata ci gaba da shawarwari da Iran watakil a cimma yarjejeniya.
Netanyahu, wanda ake tsammanin zai matsawa shugaba Trump ya fadada batutuwa da Amurka zata tattauna da Iran su hada da kayyade makamai masu linzami na kasar, ya jaddada muhimmancin a duba batun bukatun tsaron Isra’ila, amma bai nuna alamun ko shugaba Trump ya amincce da haka ba.
Shugabannnin biyu sun tattauna cikin sirri na tsawon sa’ao’i biyu da rabi, lamarin da shugaba Trump ya kira ganawa mai ma’ana, sai dai yace babu wasu muhimman batu da suka tsaida shawara akai.
Ahalinda ake ciki kuma, wata kotu a Isra’ila ta baiwa gidajen yarin kasar su baiwa falasdinawa karin abinci saboda suna jin ‘yunwa.


