A makon gobe ne ake sa ran shugaban Amurka Donald Trump zai bada sanarwar shirye shiryen sake gine Gaza da zai ci biliyoyin dala, da kuma bayanai dalla dalla na rundunar kiyaye zaman lafiya karkashin ikon MDD da za’a tura zirin, da zai bayyana zaman farko na kwamitin wanzar da zaman lafiya da ya kafa, kamar yadda wasu manyan jami’an gwamnatin suka fada a ranar Alhamis.
Ana sa ran tawagar wakilai daga kasashe 20 cikin su harda wasu shugabannin kasashe ne za su halarci zaman farko na kwamitin a ranar 19 ga watan Feburairun nan ƙarƙashin jagorancin shugaba Donald Trump, kamar yadda jami’an suka fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters kan sharadin ba za’a bayyana Sunayen su ba.
Yayinda gaggan kasashe a gabas ta tsakiya da suka hada da Turkiyya, da Masar, da Saudi Arabia, da Qatar, da wasu kasashe masu tasowa kamar Indonesia sun shiga jerin wakilai a kwamitin, amma manyan kasashen duniya da kuma fitattun kasashe a yammacin duniya suna taka-tsan-tsan.


