Tsohon Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi watsi da zargin da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi masa dangane da bacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.
A wata sanarwa da tsohon Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na Kano, Kwamared Muhammad Garba, ya sanya wa hannu, Ganduje ya bayyana zargin a matsayin mara tushe, tare da cewa yunƙuri ne na karkatar da alhakin abin da ya faru a jihar Kaduna kaɗai.
Sanarwar ta jaddada cewa Dadiyata ya rayu kuma ya gudanar da harkokinsa ne a Kaduna, inda aka san shi da sukar gwamnatin jihar a wancan lokaci.
A cewar sanarwar, babu wata hujja da ke nuna cewa ya fi mayar da hankali kan gwamnatin Kano ko kuma kan Ganduje.
Tsohon gwamnan ya buƙaci a yi nazari mai zurfi kan kalaman El-Rufai, yana mai cewa irin waɗannan manyan zarge-zarge ya kamata su kasance tare da hujjoji masu inganci, ba wai furucin siyasa kawai ba.
Ganduje ya kuma bayyana cewa jawo sunansa cikin lamarin ba tare da tabbatacciyar shaida ba na iya rikita jama’a kan batun da har yanzu bai samu cikakken bayani ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa a lokacin mulkinsa na wa’adi biyu a Kano, an san gwamnatin Ganduje da karɓar suka, hulɗa da kafafen yaɗa labarai, da kuma bai wa ’yan adawa damar bayyana ra’ayoyinsu ba tare da tsangwama ba.


