Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika

Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma
Published: February 17, 2026 at 2:06 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da wasu sabbin taraktocin noma guda 2,000 domin bunkasa aikin noma na zamani a fadin kasar tare da nufin noma sama da hekta miliyan 1.5 a duk shekara.

Ministan Noma da Samar da Abinci, Abubakar Kyari, ne ya bayyana hakan yayin bikin kaddamar da shirin a ranar Litinin a Abuja, inda ya ce wannan mataki wani gagarumin sauyi ne a bangaren noma karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cewarsa, an kaddamar da shirin ne a karkashin shirin gwamnatin tarayya na Renewed Hope National Agricultural Mechanisation Programme, wanda zai samar da taraktoci masu karfin aiki tare da na’urorin noma sama da 9,000 domin inganta yawan amfanin gona.

Ya bayyana cewa za a fara da tura taraktoci 600 a mataki na farko, sannan a biyo da wasu 750 da kuma 650 a matakai na gaba har a kai ga cika adadin 2,000 a fadin kasar nan baki daya.

Ministan ya kara da cewa ba za a bai wa mutane taraktocin a matsayin mallaka kai tsaye ba, sai dai za a mika su ga masu samar da ayyukan injinan noma (Mechanisation Service Providers), inda kowace na’ura za ta iya noma kusan hekta 600 a shekara.

Ana sa ran shirin zai taimaka wa manoma sama da miliyan 1.2 a duk fadin Najeriya, tare da inganta samar da abinci da kuma bunkasa tattalin arzikin karkara.

Hakazalika, ya ce gwamnatin ta samar da asusun tallafin noma na Naira biliyan 50 ta hannun Bankin Masana’antu domin saukaka harkokin zuba jari a fannin noma, yayin da aka kuma tanadi Naira biliyan 250 domin tallafa wa kananan manoma miliyan daya a daminar shekarar 2026.

Bugu da kari, gwamnatin ta shirya samar da motocin gyaran taraktoci guda 36, da kuma gina cibiyoyin kula da injunan noma guda bakwai a sassan kasar nan, tare da shirin kafa babbar masana’antar hada taraktoci da za ta rika samar da tsakanin guda 2,000 zuwa 4,000 a duk shekara.

Gwamnatin ta bayyana cewa wannan shiri zai taimaka wajen samar da ayyukan yi, rage wahalar aikin noma, da kuma kara yawan amfanin gona domin tabbatar da wadatar abinci a kasar nan.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi
Next Post: Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi

Karin Labarai Masu Alaka

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi
  • Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi
  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
  • Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.