A Ghana mayakan kasar ta ruwa da sama suna aikin ceto wasu masunta wadanda wasu ‘yan Bindiga da ba’a san ko su wanene ba suka kai wa hari a kwale-kwale 4 da suke ciki hari a ruwaye dake gabar ruwa a tsakiyar kasar da asuba hin ranar Alhamis, kamar yadda bayanai daga rundunar mayakan kasar da jami’an yanki suka fada.
Wata ‘yar majalisa da ta shiga jerin masu aikin ceto, tace masuntan sun gaya mata cewa an kai musu hari ne bayan da suka kwana suna kamun kifi, mutane 71 dake cikin jiragen sun tsallake rijiya da baya, amma an sace dukkan abuda suka kama da kuma kayan aikin su.
Rundunar mayakan Ghana ta bukaci jama’a su kai zuciya nesa, kuma zata bada karin bayani a yayinda take ci gaba da aikin ceton.
Da jumawa masana tafarkin tsaro akan ruwa suke daukar yankin teku da ake kira Gulf of Guinea dake iyaka da gabar ruwa ta kudacin Ghana a zaman sanannen wuri da barayin ruwa suke aika aikar su fiye da ko wani wuri a duniya.


