Fiye da mutane 50 ‘yan asalin kasar Ghana ne suka rasa rayukan su a yakin da ake fafatawa tsakanin Rasha da Ukrain, bayan da aka yaudare su suka shiga yaki, a cewar ministan harkokin kasashen waje na Ghana Samuel Okudzeto Ablakwa, bayan da ya kai ziyara Kyiv, babban birnin Ukrain, inda ake tattauna maganar daukan ‘yan Afirka yaki.
Rahotanni dake nuna jawo hankalin maza daga Afirka zuwa Rasha kan alkawarin samun aiki, amma sai su bige da yin yaki a sahun gaba sun yi yawa a watannin baya bayan nan, abinda yake jawo gurbacewar alaka tsakanin Rasha da kasashen dake da hannu a ciki.
Hukumomin Rasha sun musanta zargin daukan ‘yan Afirka ba bisa ka’ida ba don yi musu yaki.
A wani taro na manema labarai ranar Talata, da yake tsaye kusa da Alakwa, ministan harkokin wajen Ukrain Andri Sybiha, ya ce fiye da ‘yan Afirka 1780 daga kasashe 36 suke yiwa Rasha yaki.

