Dakarun Pakistan da Afghanistan sunyi arangama a wurare daban daban kan iyakokin kasashen biyu a ranar talata, har ofishin MDD a Afghanistan yake gargadin cewa an kashe farar hula 42 a Afghanistan a fadan da yanzu ya shiga kwana na shida.
Kasashen 2 da suke kudancin Asiya, wadanda ada kawaye ne kamin su zama masu gaba da juna, suna gwabza kazamin fada da basu yi haka ba cikin shekaru masu yawa, biyo bayan hari da jiragen yaki da Pakistan ta kai kan kasar cikin makon jiya, wanda yake janyo fargabar wani yaki na lokaci mai tsawo, a dai dai lokacin da yankin yake fama da hare haren Amurka da Isra’ila akan Iran.


