Zaizayar kasa, da ta auku ranar Talata bayan ruwan sama mai yawa yayi sanadiyar mutuwar mutane 200 a cibiyar ma’adanin coltan ta Rubaya dake gabashin Jamhuriyar Demokradiyar Congo, a cewar ma’aikatar ma’adanai ta kasar a ranar Laraba.
Wani babban jami’i daga kungiyar ‘yan tawaye na AFC da M23 dake rike da madafun ikon Wurin hakar ma’adanin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters a baya cewa mutane 5 zuwa 6 ne kawai suka rasu sakamakon zaizayar kasar.
Cibiyar ta Rubaya na samar da wajen kashi 15 cikin 100 na ma’adanin coltan a duniya, wanda ake sarrafa shi zuwa karfen tantalum, wanda ke iya daukan zafi me yawa, kuma masu kera wayoyin tarho da kwamputa da sassan jiragen sama na amfani da shi sosai.
Rubaya ta kasance karkashin ikon ‘yan tawayen ACF da M23 tun shekarar 2024. Wannan ibtila’in da ya faru ya biyo bayan wata daya da wani hatsarin a wajen yayi sandiyyar rayuwar mutane fiye da 200.


