Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo
Published: March 5, 2026 at 7:42 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Zaizayar kasa, da ta auku ranar Talata bayan ruwan sama mai yawa yayi sanadiyar mutuwar mutane 200 a cibiyar ma’adanin coltan ta Rubaya dake gabashin Jamhuriyar Demokradiyar Congo, a cewar ma’aikatar ma’adanai ta kasar a ranar Laraba.

Wani babban jami’i daga kungiyar ‘yan tawaye na AFC da M23 dake rike da madafun ikon Wurin hakar ma’adanin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters a baya cewa mutane 5 zuwa 6 ne kawai suka rasu sakamakon zaizayar kasar.

Cibiyar ta Rubaya na samar da wajen kashi 15 cikin 100 na ma’adanin coltan a duniya, wanda ake sarrafa shi zuwa karfen tantalum, wanda ke iya daukan zafi me yawa, kuma masu kera wayoyin tarho da kwamputa da sassan jiragen sama na amfani da shi sosai.

Rubaya ta kasance karkashin ikon ‘yan tawayen ACF da M23 tun shekarar 2024. Wannan ibtila’in da ya faru ya biyo bayan wata daya da wani hatsarin a wajen yayi sandiyyar rayuwar mutane fiye da 200.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar
Next Post: Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika
Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
Sakataren Tsaron Amurka Yace Yaki Tsakanin Amurka Da Iran Zai Dauki Sabon Salon Amurka
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
  • Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.