Ranar Laraba, koriya ta arewa ta bayyana goyon bayanta ga jama’ar Iran dangane da zaben sabon shugaban addinin kasar, Mojtaba Ali Khameni, wanda aka zaba ranar Litinin, ya gaji mahaifinsa, wanda aka kashe a farkon fara yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila, kamar yadda wata kafar yada labaran kasar ta fada.
Haka nan ma’aikatar harkokin wajen Koriya ta arewan tace, da kakkausar lafazzi tayi Allah wadai da matakan zalunci na Amurka da Isra’ila kan afkawa Iran, wadda tace haramtacciya ce, mataki da koriya ta arewan take cewa, yana rusa zaman lafiya, da ruruta rashin tabbas a duk duniya, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar ta fada.
Ahalinda ake ciki kuma, Koria ta arewa da China za su maido da zirga zirgar jirgin kasa tsakanin kasashen biyu, bayan shekaru shida, tun bayan bullar masassarar Covid 19 a shekara ta 2020. Jirgin farko daga Beijing zuwa Pyongyang zai tashi ne gobe alhamis idan Allah Ya kai mu, kuma tuni har tikiti yakare.


