Iran ta ce zata mai da martani kan harin da Amurka ta kai a cibiyar mai dake tsibirin Kharg. Fadar gwamnatin Tehran tayi kira ga mutane a Hadaddiyar Daukar Larabawa da su fice daga tasoshi da wurin ajiye jiragen ruwa, da kuma wuraren da ‘yan kasar Amurka ke boyewa, a cewar wani mai magana da yawun sojin Iran. Wani hoton bidiyo ya nuna hayaki ya turnuke a cibiyar mai ta Fujairah dake Hadaddiyar Daular Larabawa.
Iran tayi gargadin cewa zata far ma maboyun Amurkawa a Hadaddiyar Daular Larabawa, shi kuma a nasa bangaren, shugaban Amurka Donald Trump ya ce kasashe da yawa zasu aike da jiragen yaki yankin, domin a bar jiragen dakon man su wuce ta mashigin ruwa na Hormuz da Iran ta rufe. Bai yi karin bayani game da kasashen da zasu yi hakan ba, amma a wata wallafa da yayi a shafin sa na sada zumunta na Truth Social, ya ce yana fata China, Faransa, Japan, Koriya ta Kudu, Birtaniya da sauran kasashe zasu aike da jiragen yakin wajen.
Yakin da aka kusan mako uku ana fafatawa yayi sanadiyyar rayukan mutane fiye da dubu biyu, kuma ya hadddasa hargitsi irin wanda ba’a taba samun irin sa ba tarihi na samar da man fetur a duniya.


