Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
Published: March 16, 2026 at 5:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’an Amurka da ke mayar da martani kan rashin tabbas na tattalin arziki kan hauhawar farashin man fetur, a ranar Lahadi sun yi hasashen cewa, yakin Amurka da Isra’ila zai kawo karshe nan da makwanni, kuma za a samu raguwar farashin makamashi, duk kuwa da ikirarin da Iran din ta yi na cewa tana nan daram da karfi kuma a shirye take ta kare kanta.

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai karin hare-hare kan babbar cibiyar fitar da man fetur ta Iran a tsibirin Kharg a karshen mako, ya kuma ce bai shirya cimma matsaya ba don kawo karshen yakin da ya rufe mashigin Hormuz mai matukar muhimmanci tare da girgiza kasuwannin makamashi na duniya.

Jaridar Wall Street Journal ta ruwaito cewa, a farkon wannan makon ne gwamnatin Trump ta shirya yin shelar cewa kasashe da dama sun amince da kafa wata kawance don raka jiragen ruwa ta mashigin ruwa amma har yanzu suna tattaunawa kan ko za a fara gudanar da ayyukan, kafin ko bayan an kawo karshen tashin hankali, in ji jaridar Wall Street Journal, inda ta ambato wasu jami’an Amurka da ba a bayyana sunayensu ba, Sai dai Fadar White House ba ta amsa bukatar jin ta bakin nata ba.

Trump, wanda a ranar Juma’a ya ce sojojin ruwan Amurka “nan ba da jimawa ba” za su fara rakiyar jiragen dakon mai, ya ce Iran na son yin shawarwari, amma ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi a ranar Lahadi ya musanta wannan ikirarin.

Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
Next Post: Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf

Karin Labarai Masu Alaka

Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
  • China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.