Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato
Published: March 16, 2026 at 8:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Al’ummar kauyen Wanka dake karamar hukumar Kanam a Jihar Filato sun nemi hukumomi su kai musu dauki, bayan watsewarsu daga kauyen, biyo bayan kisan sojoji da ‘yan banga da ‘yan ta’adda suka yi a karshen makon jiya.

Garin Wanka, wanda ke yankin Garga a karamar hukumar Kanam a jihar Filato, na makwabtaka da karamar hukumar Alkalerin jihar Bauchi kusa da dajin da ‘yan bindiga ke cin karensu babu babbaka.

Wani mazaunin garin na Wanka da ya bukaci in sakaya sunanshi saboda tsaro, yace ‘yan bindigar sun kashe sojoji goma sha hudu da ‘yan banga biyar, lamari kenan da ya sanya suka watse daga kauyen.

Duk da cewa kafafen yada labarai sun yayata batun kisan sojojin, rundunar dake wanzadda zaman lafiya a yankin, Operation Enduring Peace bata fitar da sanarwa kan batun ba.

Bayanai sun nuna cewa sojojin da aka kashen suna aikin tabbatar da tsaro ne a yankin, kafin ‘yan bindigar su yi musu kwanton bauna suka hallaka su.

Haka ma bayanan da ba’a tantance ba sun nuna cewa sojoji sun hallaka ‘yan ta’adda fiye da ishirin a yankin na Wanka.

A wata sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa, Madam Joyce Ramnap tace gwamnati na kan bakanta na tsaron lafiyar jama’a da dukiyoyinsu.

Sanarwar tace gwamnati ta hada gwiwa da jami’an tsaro don kara azama wajen tabbatar da tsaro a dukkan yankunan dake fuskantar barazanar tsaro a fadin jihar.

Mai fashin baķi kan lamura kuma sakataren kungiyar dake raya al’ummar Kanam, Nuhu Shehu Kanam yace matsalar tsaro a yankin ba sabon abu bane amma hukumomi sun kasa shawo kanta.

Bayanai na nuni da cewa ayyukan masu bada bayanai wa ‘yan ta’adda, da aka fi sani da informants, suna tasiri wajen samun cikkas da yaki da matsalolin tsaro a yankin na Garga da kewaye.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/AUD-20260316-WA0040.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu
Next Post: Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.