A Sudan nan da mako biyu kayan jinya da ayyukan kiwon lafiya a cibiyoyin kiwon lafiyar kasar za su kare, sakamakon rikicin da ake yi a gabas ta tsakiya wadda ya janyo tsaiko na jigilar kayan jinya, muddin ba sake hanyar da aka saba bi ba, kamar yadda kungiyar tallafawa yara da ake kira Save the Chldren ta fada.
Yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran wadda yake kara bazuwa ya girgiza hanyoyin zirga zirga da jigila, saboda rufe sararin samaniyar da wasu kasashe suka yi, da kuma dakatar da jigilar kaya ta mashigin ruwan Hormuz.
Akwai magunguna da kayan Kiwon lafiya na kudi samada dala dubu dari shida wadanda ahalin yanzu suka makale a Dubai inji kungiyar da take ayyukan jinkai.
Kimanin cibiyoyin kiwon lafiya na gwamnatin Sudan 90, da suke kula da lafiyar mutane kusan dubu dari hudu sun dogara ne kan wannan kungiyar wajen samarda magunguna da sauran kayan jinya, kuma babu wata kafa a cikin kasar da zata iya samarda haka, inji wani jami’in kungiyar ta Save the Children.
Rikicin da ake yi a Sudan, tsawon shekaru uku yanzu ya raba miliyoyin jama’a da muhallansu, wadda ya haddasa mummunar yanayin zamantakewa mafi tsanani a fadin duniya.


