Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri 
Published: March 18, 2026 at 1:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 18, 2026

Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri

Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Janar O.O Oluyede, da Babban Hafsan Rundunar Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, sun isa birnin Maiduguri na Jihar Borno domin shaida yanayin da ake ciki na matsalar tsaro da kuma jajantawa al’ummar jihar Borno.

Ziyarar tasu na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 24 da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na tura dukkan hafsoshin tsaro zuwa Maiduguri, sakamakon jerin hare-haren ƴan ta’adda, ciki har da fashewar bama-bamai guda uku a yammacin ranar Litinin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane 20 tare da jikkata fiye da 100.

Shugabannin sojojin sun sauƙa a sansanin sojin sama da ke Maiduguri, inda kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta yankin Arewa maso Gabas (Operation Hadin Kai), da sauran manyan hafsoshin soji suka karɓe su.

Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na magance ƙaruwar hare-haren ƴan ta’adda a jihar Borno, musamman bayan hare-haren bama-bamai na baya-bayan nan da ake zargin mayakan Boko Haram/ISWAP ne suka kai.

Tun da farko dai, Shugaba Tinubu ya yi Allah-wadai da hare-haren, inda ya bayyana su a matsayin “ayyukan mugunta na ƙungiyoyin ta’addanci masu muguwar aniya,” tare da alƙawarin ƙara ƙaimi wajen yaƙar dukkan ƙungiyoyin ƴan ta’adda.

A halin yanzu, rundunar soji na ci gaba da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tsaro mai inganci a yankunan da abin ya shafa, ta hanyar ƙara sa ido da kuma ƙarfafa matakan tsaro.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada
Next Post: Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin

Karin Labarai Masu Alaka

Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
  • Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
  • Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.