Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas
Published: March 19, 2026 at 3:41 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 19, 2026

Babban hafsan tsaron Najeriya, Olufemi Oluyede, ya bukaci al’ummomin jihohin Borno da Yobe da su kasance dasu ake yaƙi da ta’addanci, yana mai cewa hadin kai da goyon bayan jama’a na da matukar muhimmanci wajen kawo karshen rikicin.

Oluyede ya bayyana haka ne bayan tantance ayyukan rundunar sojin Najeriya kan yaki da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP.

Ya ce binciken ya nuna cewa nasarar ayyukan soja na da alaka kai tsaye da irin hadin kan da ake samu daga al’ummomin yankin. Ya kuma yi gargadin cewa ta’addanci ba zai yi karfi ba sai da taimakon wasu daga cikin jama’a.

A cewarsa, wasu rahotanni sun nuna cewa akwai mutanen da ke taimakawa ko boye ‘yan ta’adda, abin da ke kawo cikas ga kokarin sojoji tare da tsawaita wahalar da jama’a ke ciki.

Ya kara da cewa galibin masu aikata laifukan ba baki ba ne, illa mutanen da ake sani a cikin al’umma, ciki har da makwabta da ‘yan uwa.

Don haka, ya bukaci jama’a su daina jin tsoro ko nuna bangaranci, su rika tona asirin masu laifi tare da hana su mafaka.

Oluyede ya jaddada cewa yaki da ta’addanci ba aikin soja kadai ba ne, illa aiki ne na kowa da kowa, yana kira ga jama’a su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya kuma bayar da misali da wani hari a Kukawa, inda aka gano wasu ‘yan ta’adda da suka ji rauni suna cikin al’umma, abin da ke nuna yiwuwar hadin baki.

Babban hafsan ya tabbatar da cewa rundunar soji na ci gaba da kokarin dakile sabbin dabarun ‘yan ta’adda, ciki har da amfani da jirage marasa matuki (drones).

Haka zalika, ya bukaci sarakunan gargajiya, malamai, matasa da kungiyoyin farar hula su kara taka rawa wajen wayar da kan jama’a da yakar tsattsauran ra’ayi.

A karshe, ya bukaci ‘yan kasa su kasance cikin shiri, su rika kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba, tare da tabbatar da cewa rundunar soji za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a yankin Arewa maso Gabas.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma
Next Post: Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas

Karin Labarai Masu Alaka

Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa Afrika
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
Zamu Tarwatsa Cibiyoyin Makamashi Da Cibiyoyin Mai Din Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
  • Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
  • Yayale Ahmed Ya Jagoranci Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaron Arewa Afrika
  • Kamaru Ta Lallasa Malawi 3-0, Ta Lashe Kofin WAFCON Na Farko A Tarihi Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.